Leadership News Hausa:
2025-04-27@04:01:29 GMT

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Published: 27th, April 2025 GMT

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

“Abin takaici ne ganin yadda jami’an CJTF biyu da aka kashe a ranar Juma’a, sannan kuma wasu mutane 10 da suka je daji neman itace aka kashe su yau.

“Mun riga mun birne mamatan kamar yadda addinin Musulunci ya tanada, kuma an kwashe waɗanda suka ji rauni zuwa Maiduguri domin nema musu kulawar likitoci,” in ji Sarkin.

Ya yi addu’a Allah ya jiƙan mamatan ya kuma bai wa waɗanda suka jikkata lafiya.

Sarkin ya yaba wa gwamnati da sojoji bisa ƙoƙarinsu amma ya buƙaci a ƙara amfani da sabbin fasahohin zamani da kayan yaki masu ƙarfi domin yaƙar ‘yan ta’addan.

Ya yi gargaɗin cewa waɗannan hare-hare na iya tsoratar da manoma wajen komawa gonakinsu yayin da lokacin shuka ke gabatowa.

A wani ɓangare kuma, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya sake kira ga rundunar soji da su ɗauki mataki wajen fatattakar ‘yan Boko Haram daga maɓoyarsu.

Gwamna Zulum ya yi wannan kira ne yayin da ya karɓi baƙuncin tawagar Gwamnatin Tarayya da suka haɗa da Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, da sauran manyan hafsoshin soji a gidan gwamnatin jihar da ke Maiduguri.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Boko Haram Hari

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mutum 2 ɗauke da ƙwayar tramadol ta N150m a Kano

Rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta kama aƙalla mutane biyu da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, wanda suka hada da: Muntari Shu’aibu da Imrana Rabi’u.

A wata sanarwa da Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Bakori ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana cewa an samu waɗanda ake zargin ɗauke da ƙunshi guda shida na miyagun ƙwayoyin  Tramadol da aka ƙiyasta kuɗinsu ya haura Dala 92,000 (kimanin Naira miliyan 150m).

Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe Gwamnan Kano ya kafa sabbin hukumomi 4

Bakori ya ce, “Rundunar ’yan sandan ta gudanar da wani samame ta hanyar fasaha da bayanan sirri, ta kama waɗanda ake zargin da wannan miyagun ƙwayoyin, biyo bayan wani rahoto da aka samu.”

Ya ƙara da cewa, kama wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ake yi na magance musabbabin munanan laifuka a jihar.

Ya ci gaba da cewa, “aikin ya biyo bayan ƙoƙarin da hukumar ta yi na daƙile ayyukan ta’addanci, waɗanda a cewarsa, galibin safarar muggan ƙwayoyi ne na sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a jihar.”

Kwamishinan ya kuma tabbatar da cewa an miƙa waɗanda ake zargin ga hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa reshen Jihar Kano domin ci gaba da bincike da gurfanar da su gaban ƙuliya.

“Wannan ya yi daidai da tsarin Sufeto-Janar na ‘yan sanda na aikin ‘yan sanda da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro a tsakanin ƙungiyoyin tsaro,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zulum Ya Nuna Damuwa Kan Yadda Boko Haram Ke Dawowa Wasu Yankuna A Borno
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’dda 1,770 sun kama 3,070 a Arewa —Janar Musa
  • Janyewar sojoji ke ba Boko Haram damar ƙwace yankuna —Zulum
  • An kama mutum 2 ɗauke da ƙwayar tramadol ta N150m a Kano
  • Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe
  • Zulum Ya Taya MNJTF Da Gwamnatin Alihini Bayan Harin Boko Haram A Wulgo
  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
  • Sin Da Kenya Sun Daukaka Dangantakarsu Yayin Da Xi Da Ruto Suka Gana
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen