HausaTv:
2025-04-27@14:56:36 GMT

Kasashen Duniya Sun Yi Ta AiIka Tallafi Bayan Fashewar Bandar Abbas

Published: 27th, April 2025 GMT

Ana kara samun karin ta’aziyya da kuma tallafa daga kasashen waje bayan fashewar da ta auku a tasahr jiragen ruwa na Dr Rajai a Bandar Abbasa.

Tashar talabijin ta Press Tv ta nakalto ministan harkokin cikin gida Eskandar mumunina yana fadar haka, yana kuma cewa ya zuwa yanzu, mutane 14 aka tabbatar da mutuwarsu a yaynda wasu a yayinda wasu tsakanin 700-750 suka ji rauni.

Tankar dakon mai ce ta yi binda a cikin tashar jiragen ruwan, a jiya, ammam ba’a san musabbin fashewar ba hanyanzu. Wuta ta kona tankar ta kuma tsallaka zuwa wasu kayaki kusa da wurin.

Sannan bindigan da tankar ta tayi ya watsa wutar zuwa wasu wurare daga nesa, ya fasa gilashan mutocin da suke gewaue, da wasu gine-gine.

Banda haka kasashe da dama sun yi tayin gabatar da duk wani taimako wanda gwamnatin Iran take bukata. Daga Mosco.

Firay ministan kasar Indiya Narendra Mudi ya taya Iran bakin cikin abinda ya faru, sannan yace kasar Indiya ashieye take don gabatar da tallafi.

Sauran kasashen da suka gabatar da ta’aziyya akwai  Japan, Qatar Pakisatn da sauransu, da kuma, Ammar hakim na kasar Iraki,  duk sun yi wa shugaba Pezeskiyan jajen abinda ya faru tare da tayin bada tallafi idan ta bukaci haka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Tace Ta Gamsu Da Yadda Tattaunawarta Da Amurka Yake Tafiya Zuwa Yanzu

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu ya yaba da yadda tattaunawa da Amurka kan shirin Nukliyar kasar yana tafiya kamar yadda ta dace.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto Aragchi yana fadar haka bayan, bayan ya fito daga taron tattaunawa ta ukku wanda aka gudanar a birnin Mascat na kasar Omman.

Ya ce bangarorin biyu a shirye suke su ci gaba da tattaunawa, ya kuma kara da cewa tawagra tattaunawa a wannan karon sun dan kara yawa, don akwai bukatar kwararrun a bangaren siyasa, sannan a zama mau zuwa a ranar Asabar mai zuwa zai hada kwararru a fanni makamashin nukliya.

Ministan ya kammala da cewa idan Amurka da gaske tana son hana Iran mallakar makaman Nukliya ne to yana da yakini kan cewa zamu kai ga yarjeniyar mai kyau. Ammam in ta shigar da wani ami zata samu matsala.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tace Ta Gamsu Da Yadda Tattaunawarta Da Amurka Yake Tafiya Zuwa Yanzu
  • Iran Ta Bukaci Kasashen Indiya Da Pakistan Da Hada Kai Don Yakar Ta’addanci
  • Abubuwan da suka faru yayin jana’izar Fafaroma Francis
  • Yadda Sakamakon Jawo Jarin Waje A Rubu’in Farko Na Bana Ya Ba Da Sha’awa A Kasar Sin
  • Wang Yi Ya Ce Kasar Sin Za Ta Magance Cin Zarafin Da Amurka Ke Yi Ita Kadai
  • Iran Ta Gabatar Da Tayin Shiga Tsakanin Don Sasanta Indiya Da Pakisatan
  • Rasha Ta Fara Aika Isakar Gas Zuwa Kasar  Iran Ta Azarbaijan Don Sayarwa A Kasuwannin Duniya
  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya