Aminiya:
2025-04-27@20:08:01 GMT

Ƙungiyoyin da suka yi shuhura a Firimiyar Ingila

Published: 27th, April 2025 GMT

Wannan wata mahawara ce da aka daɗe ana yi kan wace kungiya ce ta fi gawurta a Birtaniya? Shin wace kungiya ce ta fi lashe kofuna?

Wacce ce ta fi tara kudin shiga ko kuma ta fi yawan mabiya a shafukan sada zumunta?

Wace kungiya ce ta fi filin wasa mai girma? Wacce ce ta fi daraja a gasar Firimiya?

’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno Abubuwan da suka faru yayin jana’izar Fafaroma Francis

Sai dai wannan muhawara da wuya a kawo ƙarshenta, saboda dole za a ci gaba da samun ra’ayoyi mabambanta, kuma ba dole ba ne a samu gamsasshiyar amsa.

 An tafka muhawara kan abubuwa da dama, amma a ƙarshe sai muka yi nazari tare da daddale guda 10 da za mu zayyano.

a) Wannan kiyasi ne, kuma akwai ra’ayoyi mabambanta

b) Ba muna nufin cewa wannan hukunci kamar yankan wuka ba ne.

Manyan kungiyoyi 10 a Birtaniya

Manchester United Liverpool Arsenal Manchester City Celtic Chelsea Tottenham Hotspur Rangers Aston Villa Newcastle United

Domin samar da gamsasshshen bayani, mun yi nazarin kungiyoyin da suke kan gaba.

Kungiyar da ta fi lashe manyan kofi

Game da kungiyar da ta fi lashe manyan kofuna, a bisa al’ada ana kallon kungiyar da ta lashe kofuna a matsayin gawurtacciya.

Idan ana maganar lashe manyan kofuna, babu kungiyar da ta kai Celtic da Rangers.

Liverpool ce gaba a Ingila wajen lashe kofuna, sai Manchester United ke biye mata – kuma akwai alama Liverpool za ta kamo Manchester United wajen lashe gasar Premier guda 20.

Haka kuma ta fi kowace kungiya lashe gasannin Turai, sannan Arsenal ce ta fi lashe gasar FA.

Yadda Manchester City ke jan zarenta a ’yan shekarun nan, ciki har da lashe gasar premier shida a cikin shekara bakwai da lashe kofuna uku a kaka daya, wato kakar 2022-23.

Kungiyar da ta fi da yawan mabiya a kafofin sadarwa

Wasu masu tunanin mazan jiya ba za su damu da batun mabiya a kafofin sadarwa ba.

Amma suna da rawar da za su taka wajen gane kungiyar da ta fi girma ba a Ingila ba kadai, har da duniya baki daya.

Manchester United ce ta fi yawan masu mabiya a kafofin sadarwa a jimilla.

Sai dai akwai wasu kungiyoyi da suka fi mabiya a daidaikun kafofin sadarwa.

Manchester City ce ta fi karancin mabiya a kafofin sadarwa idan aka kwatanta da kungiyoyin da take makwabtaka da su, amma ta yi fintikau TikTok.

Amma kuma Tottenham ce shida a jimilla, amma kuma ta fi kowacce a TikTok.

Kungiyoyin da ake kira “manya shida” ne suka fi yawan mabiya, amma lashe gasar premier da Leicester City ta yi a kakar 2015-15 ta kara mata mabiya a kafofin sadarwa, inda ta zo ta bakwai.

Kungiyar da ta fi samun kudaden shiga

Shin batu ne ake yi na kudi? Idan kudin ake tunani, to lallai Machester City ce za ta fara zuwa a rai.

A wasu alkaluma da binciken Deloitte Money League ta fitar, ya bayyana cewa, Manchester City ce ta fi samun kudin shiga a kakar 2023-24 a Ingila da fam miliyan 708, kuma ta biyu a duniya, inda take biye da Real Madrid.

Kungiyoyin gasar premier guda tara ne suke cikin kungiyoyi 20, sannan da wasu karin biyar a cikin guda 30, saboda Brighton ta kara matsowa bayan ta fafata gasar kofin Europa a karon farko.

Kungiyar da filin wasanta ya fi girma

Idan kuma babbar kungiya na nufin mafi girman filin wasa, to lallai Manchester United ce a gaba.

Wembley ne fili mafi girma mai daukar mutum 90,000, amma Old Trafford ya fi girma a cikin filayen wasannin kungiyoyi, sannan kuma kungiyar ta sanar da shirinta na fadada filin ya zarce Wembley – inda za ta kashe fam biliyan biyu domin samar da fili mai cin mutum 100,000.

Kungiyar da ta fi karewa a matakai masu daraja a

A harkar tamaula, dadewa ana yi yana da muhimmanci. Wannan ne abin da Machester City ta ce a shekara 10 da suka gabata.

Ta ce gasar premier guda shida – har da lashe guda hudu a jere. Yanzu tana da kiyasin 1.7.

A tsakanin Liverpool da Manchester United da Arsenal da Tottenham da Chelsea babu takamaiman bambanci a matsakaici matsayi.

Da West Ham da Everton da Crystal Palace sun fi kwaarewa a tsakankanin tsakiyar teburi a shekara 10 da suka gabata.

Ba a saka Celtic da Rangers ba saboda ba sa buga Gasar Premier, amma Celtic ta kare a ta daya sau tara a shekara goma da suka gabata, sannan ta kare a ta biyu a 2020-21, ga Rangers, wadda ita kuma ta kasance ta biyu sau biyar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Firimiyar Ingila mabiya a kafofin sadarwa Kungiyar da ta fi kungiyar da ta fi gasar premier lashe gasar

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe sojoji 12 a barikin Nijar

An kashe sojoji 12 a yankin Tillaberi na yammacin ƙasar mai iyaka da Mali da Burkina Faso, yankin da ke zama tungar masu iƙirarin jihadi da ’yan ina da kisa masu nasaba da ’yan ƙungiyoyin al Qaeda da IS.

Ma’aikatar tsaron Nijar ta sanar da cewa an yi wa dakarunta na bataliyar ko-ta-kwana mai suna Almahao kwanton ɓauna ne a wani kauye da ke kusa da Sakoira na yammacin Tillaberi, inda sojan suka jima suna ɓarin wuta da ’yan ta’adda kafin a kawo musu ɗauki.

An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa

Gwamnatin ta bayyana cewa tuni ta cafke mutane biyu da ake zargi da kai harin a barikin sojojin da ke da nisan mil shida daga ƙauyen Sakoira a jihar ta Tillaberi.

A baya gwamnatin ƙasar ta sanar da kashe ’yan ta’adda tara, ta kuma ƙwace makamai daga hannu masu iƙirarin jihadi da suka kai wani harin da ta daƙile a yankin.

A yankin Tahoua mai iyaka da Nijeriya, rundunar tsaron Nijar ɗin ta sanar da ɗauki ba dadi da Lakurawa masu yawan yin kutse kuma suna kai hari ga bututun man fetur ɗinta da ke zuwa gaɓar teku a Benin.

Nijar Mali da kuma Burkina faso sun shafe sama da shekaru 10 ƙarƙashin barazanar ƴan ta‘adda masu iƙirarin jihadi da ke afkawa jami’an tsaro da kuma fararen hula lokaci zuwa lokaci.

To sai dai kuma ƙididdiga ta nuna ƙaruwar kai hare-hare tun bayan da sojojin ƙasashen uku suka yanke shawarar kifar da gwamnatin fararen hula.

Rikicin yankin Sahel da ya samo asali daga ƙasar Mali a 2012, wanda kuma ya faɗaɗa har zuwa ƙasashen Burkina Faso da Nijar da kuma Benin da ya halaka dubban mutane kama daga sojoji har zuwa farar hula.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Liverpool Sun Zama Zakaran Gasar Premier Bayan Lallasa Tottenham
  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar
  • An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba
  • Tashin Gobara A Tashar Jirgi Ruwa Na Shahid Raja’i Da Ke Kudancin Iran Ya Lashe Rayukan Mutane A Kudancin Iran
  • Wace Kungiya Ce Za Ta Lashe Kofin Zakarun Turai?
  • Yanzu Ne Lokacin Da Arsenal Ya Kamata Ta Lashe Kofin Zakarun Turai – Walcott
  • Gwamna Radda Ya Gargadi Ƴan NYSC Kan Shiga Ƙungiyoyin Asiri
  • Shin Manchester United Za Ta Iya Lashe Kofin Europa League?
  • Amurka Ta Yi Barazana Ga Ukraine A Dai-dai Lokacinda Ta Fitar Da Shirin Zaman Lafiya Da Rasha Na Karshe