HausaTv:
2025-04-27@22:09:47 GMT

 Nigeria: Boko Haram Ta Kashe Mutane 12 A Borno

Published: 27th, April 2025 GMT

‘Yan kungiyar ta boko haram sun kashe masu sintiri farafen hula 2 da kuma wasu sana’ar yin sarar itace  su 10 a  a Bokko Gjide a karamar hukumar Gwoza dake Jahar Borno. Sarkin Gwoza Alhaji Muhammad Shehu Timta ya tabbatar da kisan mutanen da aka fi kira da (Civilian JTF) bayan da aka yi musu kwanton bauna a kan hanyar Kirawa.

Haka nan kuma ya kara da cewa; mutanen sun shiga cikin daji ne domin saro itace, a ranar Asabar, a yayin da masu dauke da makaman su ka yi musu kwanton bauna su ka kashe kashe daga cikinsu, sannan kuma su ka yi wa wasu biyu munanan raunuka.

Sarkin ya kara da cewa; Mun yi jana’izar 10 daga cikinsu sannan kuma mu ka dauke wadanda su ka jikkata zuwa Maiduguri domin samun magani.

Wannan harin na Boko Haram ya afku ne bayan sa’o’i 48 da shugaban kasar Bola Ahmad Tinubu ya aike da ministan tsaro Badaru Abubakar, da kuma babban jami’in tsaro na soja Janar Christopher Musa, domin su yi bitar halin tsaro da ake ciki a Jahar ta Borno.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum Ya Taya MNJTF Da Gwamnatin Alihini Bayan Harin Boko Haram A Wulgo

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
  • Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare
  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno
  • Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
  • Zulum Ya Nuna Damuwa Kan Yadda Boko Haram Ke Dawowa Wasu Yankuna A Borno
  • Janyewar sojoji ke ba Boko Haram damar ƙwace yankuna —Zulum
  • Zulum Ya Taya MNJTF Da Gwamnatin Alihini Bayan Harin Boko Haram A Wulgo
  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza