Leadership News Hausa:
2025-04-28@01:12:09 GMT

Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara

Published: 27th, April 2025 GMT

Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara

Ƴan fashi sun sace fasinjoji guda bakwai a cikin motocin haya biyu a ƙauyen Eleyin da ke cikin ƙaramar hukumar Isin a Jihar Kwara.

A cewar rahoton LEADERSHIP, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:45 na yamma a ranar Juma’ar da ta gabata, lokacin da wasu ƴan fashi su biyar suka toshe hanya, suka tsayar da motoci biyu, sannan suka tilasta ɗaukar dukkanin fasinjojin zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Uwargidan Shugaban Kasar Sin Ta Tattauna Da Takwararta Ta Kasar Kenya Ra’ayin Matasa Kan Kungiyar ‘Yan Ta’adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa, daga cikin fasinjojin motar ɗaya, akwai shugaban sashin shari’a na ƙaramar hukumar Oke Ero, Barr. Elizabeth Arinde, da daraktan gudanar da ma’aikata na wannan ƙaramar hukumar, Alh. Musbau Amuda.

Kakakin Ƴansanda na Jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa an sami ceto fasinjoji biyu, Ganiyu Ajayi da Kolawole Adeyemi. Ta kuma ƙara da cewa, har yanzu ana ƙoƙarin ceto sauran fasinjojin guda biyar da kuma kama ƴan fashin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno

Mayakan Boko Haram sun halaka mutum goma sha biyu da jikkata karin biyu bayan wani hari da suka kai kan kauyen Bokko Ghide a Karamar Hukumar Goza ta Jihar Borno.

Wakilinmu ya ruwaito cewa cikin wadanda aka kashe akwai ’yan sa-kai biyu da wasu mutum 10 da suka fita debo itacen girki.

Sulhu da ’yan bindigar Katsina: Gaba aka ci ko baya? Abubuwan da suka faru yayin jana’izar Fafaroma Francis

Sarkin Gwoza, Alhaji Mohammed Shehu Timta, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce mayakan sun yi wa ’yan sa-kan kwanton bauna a kan hanyar Kirawa da ke gudunmar Pulka.

“Sun fita neman itace ne a jeji a ranar Asabar, yayin da yaran [mayakan Boko Haram] suka yi musu kwanton bauna, inda suka kashe mutum 10 sannan wasu suka ji munanan raunuka.

“Mun binne mutum 10 sannan biyu da suka jikkata an mika su asibiti.

“Abin takaici shi ne biyu daga cikin yan sa-kai sun sadaukar da rayuwarsu wajen kare mutanenmu wadanda aka kashe ranar Juma’a.”

Bayanai sun ce harin ya auku ne yayin da ake kokarin ganin an mayar da jama’ar yankin garuruwansu don su ci gaba da rayuwa, bayan kwashe shekaru da dama suna gudun hijira a wasu wurare saboda hare-haren na ’yan Boko Haram.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴansanda Sun Damke Ango Da Abokansa Bayan Mutuwar Amarya A Jigawa
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno
  • ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Sun Yi Kira Ga Kungiyoyin Kasa Da Kasa Da Su Ceto Yara Da Tsofaffi Daga Mummunan Kangi A Sudan
  • Yanzu Ne Lokacin Da Arsenal Ya Kamata Ta Lashe Kofin Zakarun Turai – Walcott
  • Gwamna Radda Ya Gargadi Ƴan NYSC Kan Shiga Ƙungiyoyin Asiri
  • Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya
  • Hajji 2025: Hukumar Alhazan Yobe ta gudanar da taro don mahajjata
  • An sako limamin Katolika da aka sace a Kaduna
  • An Sako Malamin Kiristan Cocin Katolika Da Aka Sace A Kaduna