Aminiya:
2025-04-28@15:44:16 GMT

Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi

Published: 28th, April 2025 GMT

Wani wanda ake zargi da safarar sassan jikin ɗan Adam ya shaida wa jami’an tsaro cewa ya shafe sama da shekara 10 yana sayar da sassan jikin mutum don samun kuɗi.

Dubun mutumin sun cika ne a ranar Asabar din da ta gabata inda sojoji suka kama shi a yankin Kulanla Odomoola da ke Jihar Ogun.

A furucinsa da ya amsa laifin, wanda ake zargin ya amince da sayar da sassan jikin mutum ga masu buƙata don samun kuɗin shiga.

“Na dogara ne da sayar da sassan jikin mutum tsawon shekaru 10 da suka gabata. Yawancin sassan da nake sayarwa ina tono su ne daga sabbin kaburbura a makabartu, yayin da wasu kuma nake samun su daga gawarwakin da aka watsar a gefen hanyoyi,” in ji shi.

Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”

Wanda ake zargin, wanda ya amsa laifinsa ga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi kafin sojoji su cece shi, ana zargin yana kan hanyarsa ne na kai wani sassan jiki ga wani mai siye lokacin da aka kama shi.

Daga nan aka miƙa wanda ake zargin ga ’yan sanda a yankin Noforija don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

Laftanar Kanar Olabisi Olalekan Ayeni, Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 81, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayan kama wanda ake zargin daga baya an miƙa shi tare da kayayyakin da aka samu a wurinsa, ga ’yan sandan Najeriya don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

“Sojojin sun ceto wanda ake zargin daga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tsaro sayar da sassan jikin wanda ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar ya da umarnin fara duban watan Zulki’ida na shekarar 1446 daga gobe Lahadi, 29 ga watan Shawwal, wanda ya yi daidai da 27 ga watan Afrilun 2025.

Hakan na ƙunshe cikin wata takarda da Wazirin Sakkwato kuma shugaban kwamitin bai wa majalisar Sarkin Musulmi shawara kan harkokin addinin musulunci, Farfesa Sambo Wali Junaid ya raba wa manema labarai.

Sarkin Musulmi ya ce duk wanda ya samu ganin jinjirin watan ya sanarwa hakimi ko uban ƙasa mafi kusa da shi don sanar da majalisar sarkin musulmi.

A ƙarshe sanarwar ta ce Sarkin ya roƙi Allah Ya kawo wa Nijeriya zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samarin Arewa sun yaba wa Sarkin Daura kan bai wa Ja’o’ji muƙami
  • An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba
  • Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa
  • Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
  • Sulhu da ’yan bindigar Katsina: Gaba aka ci ko baya?
  • A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin Musulmi
  • ’Yan kasuwar da suka ɓoye kayan abinci na tafka asara
  • A Karon Farko A Tarihi Adadin Lantarki Da Sin Ke Iya Samarwa Ta Karfin Iska Da Hasken Rana Ya Zarce Wanda Ake Iya Samarwa Ta Amfani Da Dumi
  • An sako limamin Katolika da aka sace a Kaduna