Leadership News Hausa:
2025-04-28@23:19:42 GMT

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

Published: 28th, April 2025 GMT

Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi

Gwamnatin tarayya ta ɗauki nauyin dukkanin buƙatun ɗaliban na zana jarabawar, ciki har da abinci da wurin kwana, har na tsawon kwanaki uku. Kwamishinan ilimi na jihar Bauchi, Dakta Lawal Mohammed Rimin Zayam, ya yaba da wannan mataki na JAMB, yana mai kira ga iyaye da su tura ‘ya’yansu dake da lalura ta musamman makaranta domin samun ilimi.

Kwamishinan ya kuma yi kira ga al’umma da iyaye su fahimci muhimmancin ilimi, musamman ga yara masu naƙasa, yana mai cewa gwamnati za ta ci gaba da wayar da kan iyaye don ganin suna tura ‘ya’yansu makaranta.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jarrabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Radda Ya Gargadi Ƴan NYSC Kan Shiga Ƙungiyoyin Asiri

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya gargaɗi sabbin masu yin hidimar ƙasa (NYSC) da aka tura zuwa jihar da su guji shiga ƙungiyoyin sirri, da ayyukan siyasa, da kuma nuna kiyayyar addini a duk tsawon lokacin hidimarsu.

A cikin jawabin gwamnan, wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan jihar Abdulkadir Mamman Nasir, ya gabatar a yayin shirin gabatar da ƴan hidimar na rukunin A, na tsari na ɗaya, Gwamna Radda ya bayyana cewa wannan horon na farko wani muhimmin mataki ne a tafiyar hidimar ƙasa da mambobin NYSC ke yi.

Masu Garkuwa Sun Nemi Fansar Miliyan 250 Kafin Su Saki Tsohon Shugaban NYSC, Janar Tsiga Minista Ya Nemi A Mayar Da  NYSC Shekaru 2

Ya kara da cewa suna buƙatar su kasance cikin tsari na miƙa wuya ga alƙawarin da suka ɗauka yayin shiga aikin, yana mai tabbatar da cewa za su sami yanayi mai kyau a tsawon horon da za su yi, tare da ƙarfafa musu gwuiwa su shiga cikin dukkanin ayyukan sansanin.

Gwamna Radda ya jaddada mahimmancin kiyaye dabi’un NYSC da kuma ganin shekarar hidimar a matsayin daraja ga kasa, yana mai cewa su guji shiga dukkanin al’amuran da ka iya kawo rashin zaman lafiya a cikin al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
  • Ribar Wasu Manyan Kamfanonin Masana’antun Sin Ta Karu Da 0.8% a Farkon Watanni Uku Na Bana
  • Iran ta Bayyana cewa: TattaunawarMuscat Wata Dama Ce Ta Samun Zaman Lafiya Kan Batutuwan Masu Sarkakiya
  • Zulum Ya Nuna Damuwa Kan Yadda Boko Haram Ke Dawowa Wasu Yankuna A Borno
  • Gwamna Radda Ya Gargadi Ƴan NYSC Kan Shiga Ƙungiyoyin Asiri
  • Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
  • ’Yar Arewa da ta kafa tarihin samun Digiri Mai Daraja ta ɗaya a fannin Shari’a
  • 2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed