Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
Published: 29th, April 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana a yau Litinin cewa, babu wata tattaunawa da aka yi ta wayar tarho tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka a baya-baya nan, haka kuma bangarorin biyu ba su cimma wata yarjejeniya ko su tuntubi juna game da batun haraji ba. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare.
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Tace Ta Gamsu Da Yadda Tattaunawarta Da Amurka Yake Tafiya Zuwa Yanzu
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu ya yaba da yadda tattaunawa da Amurka kan shirin Nukliyar kasar yana tafiya kamar yadda ta dace.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto Aragchi yana fadar haka bayan, bayan ya fito daga taron tattaunawa ta ukku wanda aka gudanar a birnin Mascat na kasar Omman.
Ya ce bangarorin biyu a shirye suke su ci gaba da tattaunawa, ya kuma kara da cewa tawagra tattaunawa a wannan karon sun dan kara yawa, don akwai bukatar kwararrun a bangaren siyasa, sannan a zama mau zuwa a ranar Asabar mai zuwa zai hada kwararru a fanni makamashin nukliya.
Ministan ya kammala da cewa idan Amurka da gaske tana son hana Iran mallakar makaman Nukliya ne to yana da yakini kan cewa zamu kai ga yarjeniyar mai kyau. Ammam in ta shigar da wani ami zata samu matsala.