Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
Published: 29th, April 2025 GMT
Wasu abubuwan fashewa da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram ne suka dasa, sun kashe kimanin mutane 26, ciki har da mata da ƙananan yara a kusa da garin Rann da ke Ƙaramar Hukumar Kala Balge ta Jihar Borno.
Majiyoyin tsaro da na cikin gari sun bayyana cewa mutane da dama sun jikkata bayan da motar da ke ɗauke da wadanda abin ya shafa zuwa Gambarou Ngala ta taka abin fashewar.
Wata majiya ta ce, “Ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba, amma rahotanni na farko sun nuna cewa mata huɗu da yara shida da maza 16 ne suka mutu a wannan fashewar.”
Ta ci gaba da cewa lamarin ya faru ne a kan hanyar Furunduma, kimanin kilomita 11 daga garin Rann, da misalin karfe 11 na safe a ranar Litinin.
Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin NajeriyaTa ƙara da cewa an kai wasu da suka jikkata asibitin Rann domin kula da su.
Babu wata sanarwa a hukumance daga bangaren sojoji ko ’yan sanda game da faruwar lamarin.
Sai dai kuma, kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Borno, Kenneth Daso, bai yiwu ba saboda layin wayarsa ba ya shiga.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Abubuwan Fashewa Boko Haram mata da ƙananan yara Rann Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno
Wata majiya kuma ta bayyana cewa adadin mutanen da suka mutu na iya fin haka, duba da yawan mata da yara da lamarin ya rutsa da su.
A lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomin soji da ‘yansanda ba su fitar da wata sanarwa ba dangane da lamarin ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp