Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
Published: 30th, April 2025 GMT
Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya kaddamar da ayarin likitoci su tara domin kula da lafiyar maniyata aikin hajjin na wannan shekaran.
Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan bayan ganawar farko da ayarin da kuma shugabannin hukumar.
Ayarin likitocin ƙarƙashin jagorancin Dr.
Sannan kuma za su bayar da taimakon gaggawa a kasar Saudiyya tare da haɗin gwiwar Ayarin likitocin daga Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON).
Shugaban hukumar ya ce mambobin ayarin za su kasance cikin tsari na duba lafiyar mahajjata a tsawon lokacin aikin hajjin.
“Lafiya maniyata aikin hajjin tana da matuƙar muhimmanci, mun zaɓi ayarin ne bisa ƙwarewarsu, kuma muna da tabbacin za su bayar da ingantaccen kulawa ta lafiya a lokacin aikin hajjin,” In ji shi.
Shugaban ya ƙara da cewa za a gudanar da cikakken gwajin lafiya ga dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajj, musamman don gano mata masu juna biyu.
“Babu sassauci ko kaɗan wajen barin mata masu juna biyu su tafi Hajj.” in ji Malam Salihu, yana mai jaddada cewa gudunmuwar da ayarin likitocin za su bada wajen tabbatar da wannan doka, na da muhimmanci don bin ƙa’idodin aikin Hajjin.
Ya ja hankalin ayarin likitocin su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa da sadaukarwa, domin tabbatar da cewa mahajjata sun samu aikin hajji mai sauƙi cikin koshin lafiya.
Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: ayarin likitocin
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya
Ministan kiwon lafiya na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Muhammad Ridha Zafarqandi ya tattauna hanyoyin bunkasa aiki tare a fagen kiwon lafiya da mataimakin ministan kiwon lafiya na tarayyar kasar Rasha.
Ministan na Iran dai ya yi wannan trattaunar ne a jiya Lahadi inda su ka tabo fagage da dama da su ka yi tarayya akansu a cikin harkar kiwon lafiya.
Ministan na Iran ya kuma ce, a baya kasashen biyu sun cimma yarjejeniya wacce a wannan lokacin ake son bunkasa ta.
Muhammmad Ridha Ya kuma bayyana yadda kasashen biyu suke da kayan aiki masu yawa a fagagen magance cutuka masu yaduwa da wdanda ba su yaduwa haka nan kuma fagen yin magunguna.
Shi kuwa mataimakin ministan kiwon lafiyar na tarayyar Rasha Olog Silgy ya tabbatar da cewa,kasarsa a shirye take ta bunkasa aiki da jamhuriyar musulunci ta Iran a fagen musayar dalibai da kuma nazarce-nazarce da bincike na ilimin likitanci.
Kasashen biyu sun kafa kwamitin hadin gwiwa na yin fada da cutuka masu yaduwa da zai taka rawa mai girma wajen magance cutuka.