Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ta Saki Bafalasdine Mafi Dadewa A Gidan Yarinta
Published: 26th, January 2025 GMT
Bayan tsawon shekaru 40 a tsare, shugaban fursunonin Falasdinawa, Mohammed Al-Tous, ya samu ‘yancinsa
Kungiyar kula fursunonin Falasdinawa da suke tsare a gidan yarin haramtacciyar kasar Isra’ila ta bayyana cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila ta saki Muhammad al-Tous, wanda shi ne fursuna mafi tsufa a hannunta, tare da tasa keyar shi tare da wasu fursunoni 69 zuwa kasar Masar, a wani bangare na yarjejeniyar musayar fursunoni tsakaninta da kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas.
A ranar Asabar din da ta gabata ne gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta saki fursunonin Falasdinawa 200 a madadin wasu mata sojoji hudu da kungiyar Hamas ke tsare da su a Zirin Gaza.
Al-Tous (mai shekaru 69) yana tsare tun 1985 kuma yana cikin kungiyar Fatah an yanke masa hukuncin daurin rai da rai kuma ya shafe shekaru 40 a jere a gidajen yarin haramtacciyar kasar Isra’ila.
An kama Al-Tous ne bayan an fafare shi a lokacin da yake cikin wata mota ta kungiyar Fatah da ta kai hare-hare da dama kan wasu wurare da dama a haramtacciyar kasar Isra’ila a yankin Beit Laham.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Dakatar Da Shugaban Ma’aikatan jihar Kano
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da Muƙaddashin Shugaban Ma’aikata kuma babban Sakatare na sashin shirye-shirye, Salisu Mustapha, bisa zargin yin kutse a albashin ma’aikatan gwamnati da rashin biyan wasu daga cikinsu.
A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar daren Alhamis, an bayyana cewa dakatarwar ta fara aiki nan take, tare da umartar Mustapha da ya sauka daga matsayin babban Sakatare don bai wa kwamitin bincike damar gudanar da aikinsa ba tare da katsalandan ba.
Labarin Bukar, Malamin Da Ya Shafe Watanni 20 Ba Tare Da Albashi Ba A Borno Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Zaftare Albashin Ma’aikataA don ci gaba da gudanar da harkokin ofishin, gwamnan ya nada Malam Umar Muhammad Jalo, Babban Sakatare na bincike, kimantawa da tsare-tsare (REPA), a matsayin sabon muƙaddashin shugaban ma’aikata har sai an kammala bincike.
Wannan matakin na zuwa ne bayan kafa kwamitin mutum bakwai ƙarƙashin Hon. Abdulkadir Abdussalam da ke da wa’adin kwanaki bakwai don gano gaskiyar lamarin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp