Babban kwamandan sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Atisayen soji na “Manzon Allah Mai Girma na 19” ya cimma gagarumar nasara

Babban kwamandan sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Admiral Ali Reza Tangsiri ya sanar da cewa: Atisayen soji mai take “Manzon Allah Mai Girma na 19” ya cimma gagarumar nasara da burin da ake son kai wa bayan samun nasarar gwada sabbin na’urori da gudanar da ayyuka daban-daban, tare da samun nasarar gwajin kai hari kan wuraren abokan gaba.

A wata hira da ya yi da manema labarai a yau Lahadi, Admiral Tangsiri ya bayyana cewa: A rana ta biyu ta atisayen “Manzon Allah Mai Girma na 19” da aka gudanar na gwada karfin soji, wanda ke dauke da sunan shahidi Manjezi, makamai masu linzami daga kasa zuwa teku da kuma daga kasa zuwa masu cin dogon zango, matsakaici da gajere.

Ya kara da cewa: A cikin wannan atisaye a karon farko an harba makami mai linzami na Nawab da ke goyon bayan shamakin jirgin sama da jirgin ruwan shahidi Qassim Suleimani kuma sun samun nasarar cimma wurin da aka harba su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Arakci: Abokan Gaba Za Su Yi Nadamar Yi Wa Iran Barazana

Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Arakci ya bayyana cewa, duk wata barazana da za a yi wa Iran za ta sa makiya su yi babbar nadama.

A wata hira a tashar talabijin din almasirah ta kasar Yemen ta yi da shi, ministan harkokin wajen na Iran  ya ce, farfagandar da ake yi ta cewa, kai wa kasar Yemen hari  share fage ne na yaki da Iran ba sabon abu ba ne, an sha yin irin wannan barazanar a baya.

Abbas Arakci ya kara da cewa; Iran ba za ta taba kyale duk wani mahaluki da zai rika yin Magana da ita da harshe na barazana ba, sannan ya kara da cewa makiya za su yi nadamar wannan barazanar.

Da yake Magana akan cigaba da kai wa Yemen hare-hare da Amurkan take yi, ministan harkokin wajen na Iran ya ce, nasarar da Yemen din take samu ne ya sa hakan take faruwa,kuma a cikin shekaru 10 na hare-haren da ake kai wa Yemen har yanzu an kasa yin galaba akan ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu dokar da na karya saboda yin taro a mazaɓata — Natasha
  • Babu dokar da na karya saboda yin taron a mazaɓata — Natasha
  • Sojojin Yemen Sun Harbo Jirgin Leken Asirin Amurka Samfurin MQ9
  • BUK ta ƙaddamar da Sabuwar Manhajar Duba Sakamako Jarabawa
  • Gwamna Abba Ya Nemi A Bayyana Fuskokin Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Arakci: Abokan Gaba Za Su Yi Nadamar Yi Wa Iran Barazana
  • Sin Ta Gano Babban Yankin Hakar Danyen Mai A Tekun Kudancin Kasar
  • Somalia: Harin Amurka a kan kungiyar IS ya kashe wasu mambobin kungiyar
  • Eidl Fitr: Gwamna Dauda Lawal Ya Buƙaci A Samu Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
  • Hezbulla: Iran Ce Babbar Mai Goyon Bayan Al-Ummar Falasdinu