Babban kwamandan sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Atisayen soji na “Manzon Allah Mai Girma na 19” ya cimma gagarumar nasara

Babban kwamandan sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Admiral Ali Reza Tangsiri ya sanar da cewa: Atisayen soji mai take “Manzon Allah Mai Girma na 19” ya cimma gagarumar nasara da burin da ake son kai wa bayan samun nasarar gwada sabbin na’urori da gudanar da ayyuka daban-daban, tare da samun nasarar gwajin kai hari kan wuraren abokan gaba.

A wata hira da ya yi da manema labarai a yau Lahadi, Admiral Tangsiri ya bayyana cewa: A rana ta biyu ta atisayen “Manzon Allah Mai Girma na 19” da aka gudanar na gwada karfin soji, wanda ke dauke da sunan shahidi Manjezi, makamai masu linzami daga kasa zuwa teku da kuma daga kasa zuwa masu cin dogon zango, matsakaici da gajere.

Ya kara da cewa: A cikin wannan atisaye a karon farko an harba makami mai linzami na Nawab da ke goyon bayan shamakin jirgin sama da jirgin ruwan shahidi Qassim Suleimani kuma sun samun nasarar cimma wurin da aka harba su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu

Kakakin Majalisar dinkin MDD Stephane Dujarric ya bada sanarwan cewa yana makaranta a Gaza fiye da 100,000 suka fara karatu a makarantu a yankin a ranar 23 ga watan Fabrayrun da muke ciki.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jami’in MDD yana fadar haka a jiya Alhamis kwanaki huda da fara karatu a yankin na Gaza, bayan tsekon da aka samu saboda yakin da HKI ta dorawa kasar na tsawon shekara guda da watanni.

Dujarric ya bayyana cewa a halin yanzu makarantu 165 suka bude kofofin su ga yan makaranta a gaza, kuma ga mafi yawansu wannan shi ne karo na farko da suka shiga aji a cikin watanni 16 da suka gabata.

Jami’an gwamnati a Gaza sun bayyana cewa HKI ta rausa kashi 85% na makarantun Gaza a cikin yakin da ta dorawa yankin daga cikin watan Octoban shekara ta 2023.

Labarin ya kara da cewa akalla daliban makaran 12,800 da malaman makaranta  da ma’aikatan makarantu 800 suka rasa rayukansu a yankin na shekara guda da watanni. Sannan HKI ta rusa cibiyoyin karatu akalla 1,166 a wannan yakin. Banda haka yakin ya jawo asarar dalar Amurla billiyon $2 wa bangaren ilmintarwa a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yan Ta’adda Sun kashe Sojojin Sa Kai Na Basij Biyu A Yankin Kudu Maso Gabacin Kasar Iran
  • Ta ina Kungiyar Hizbullah ke samun kuɗaɗenta?
  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1
  • MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu
  • Hukumar Alhazai Ta Kaduna Ta Nemi Goyon Bayan Sarkin Zazzau Don Nasarar Aikin Hajjin Bana
  • An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya
  • LEADERSHIP HAUSA Ta Bayyana Wadanda Suka Yi Nasara A Gasar Gajerun Labaran Soyayya
  • Iran Ta Yi Tir Da Kakkausar Murya Kan Barazanar Soji Da Isra’ila Ke Yi Mata
  • 7 Oktoba : Sojin Isra’ila Sun Amince Da “Cikakkiyar Gazawa” A Harin Hamas
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki