✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC

Sabon rahotonta na wata-wata da ta fitar a ranar Litinin ya ce yawan man da Nijeriya ta samar ya ragu zuwa ganga miliyan 1.40 a…

Rahoton Kungiyar Kasashe Masu Samar da Man Fetur (OPEC) ya nuna cewa Nijeriya ta ci gaba da riƙe matsayinta na ƙasa mafi yawan samar da ɗanyen man a nahiyar Afirka a watan Maris.

OPEC ta ce hakan ya faru ne duk da raguwar yawan man da ƙasar ta samar a watan da ya gabata.

Sabon rahotonta na wata-wata da ta fitar a ranar Litinin ya ce yawan man da Nijeriya ta samar ya ragu zuwa ganga miliyan 1.40 a kowace rana a watan Maris, idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.46 a kowace rana a watan Fabrairu.

A cewar rahoton, duk da raguwar, yawan man da Nijeriya ta samar shi ne mafi yawa a Afirka, inda ya zarce Algeria da Congo.

OPEC ta kara da cewa ta hanyar ci gaba da ƙarfin da ta samu a watan Fabrairu, Nijeriya ta zarce Algeria, wacce ta samar da ganga 909,000 a kowace rana, da kuma Congo, wacce ta samar da ganga 263,000 a kowace rana.

Ta ci gaba da da cewa Nijeriya ta samar da ganga miliyan 1.51 a kowace rana a watan Maris, idan aka kwatanta da ganga miliyan 1.54 a kowace rana a watan Fabrairu.

Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Sama ta Nijeriya (NUPRC) ta ce yawan man da ƙasar ta samar ya ragu zuwa ganga 1,400,783 a kowace rana a watan Maris.

Duk da raguwar yawan man da aka samar a watan Maris, NUPRC ta ce matsakaicin yawan ɗanyen man da aka samar ya kai kashi 93 cikin ɗari na adadin ganga miliyan 1.5 da OPEC ta ware wa Nijeriya.