Aminiya:
2025-04-21@06:49:17 GMT

’Yan sanda sun yi ƙarin haske kan barazanar harin ’yan ta’adda a Kano

Published: 27th, January 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta yi ƙarin haske dangane da barazanar harin ’yan ta’adda da ta yi gargaɗin aukuwarsa a bayan nan.

Da yake yi wa manema labarai jawabi, Kwamishinan ’Yan sandan Kano, Salman Dogo Garba, ya ce sun ɗauki matakan da suka dace biyo bayan barazanar harin ’yan ta’adda musamman a yayin taron Maulidin Shehu Ibrahim Inyass na ƙasa da aka gudanar ranar Asabar a jihar.

Ɗan shekara 30 ya mutu a kududdufi a Kano ’Yan majalisa sun nemi cin hancin N480m kafin amincewa da kasafin jami’o’i —Bincike

“Mun ankarar da jama’a sannan muka ɗauki matakan da suka dace domin tunkarar lamarin,” in ji CP Garba.

Ya bayyana cewa wasu daga cikin waɗanda ake zargin dangane da lamarin sun tsere daga jihar a sakamakon bayanan sirri da rundunar ta tattara.

“Mun kuma samu nasarar cafke wani mutum guda da ya shigo Kano ya samu mafaka a wani coci.

“Haka kuma mun samu ababen fashewa da sauran kayayyakin da aka yi yunƙurin kai harin da su,” a cewar CP Garba.

Kwamishinan ya jaddada muhimmancin tattara bayanan sirri domin daƙile duk wata barazana da ƙoƙarin haɗin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da tsaro.

CP Garba ya kuma yi tsokaci irin ƙalubalen da suke fuskanta dangane da yadda ake siyasantar da duk wani lamari musamman a wurare irin Jihar Kano, sai dai ya nanata cewa za su ci gaba da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na tabbatar da kiyaye da doka da oda.

“Komai sai an siyasantar da shi a Jihar Kano hatta abincin da muke ci. Sai dai ina ƙara tabbatar da cewa rundunar ’yan sandan da nake jagoranta ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da tsaro a jihar nan.

“Tun daga kan iyaye da kakanni nake cikin ɗariƙar Tijjaniyya saboda haka ba zan gushe ba wajen zama jakada na zaman lafiya da tabbatar da tsaro ba.

Kwamishinan ya ƙara tabbatar wa al’ummar jihar cewa rundunar ’yan sandan za ta ci gaba faɗi tashin domin daƙile duk wata barazana da za ta kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron jihar.

Ya buƙaci al’umma da suka kasance masu lura da sanya ido domin bai wa hukumomin tsaro haɗin kai na tabbatar da tsaro a jihar.

Ya kuma miƙa godiya ga duk waɗanda suke bai wa jami’an tsaro goyon baya na wanzar da aminci a jihar.

A bayan nan ne dai aka zargi rundunar ’yan sandan jihar da yunƙurin hana gudanar da Maulidin Shehu Inyass na ƙasa bayan gargaɗin da ta yi kan barazanar harin ’yan ta’adda a jihar.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda yan ta adda Jihar Kano tabbatar da tsaro barazanar harin yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji

“Amfani da haraji a matsayin makami don matsin lamba da son rai yana nuni da tsarin siyasa na rashin haɗin kai da kare tattalin arziƙi da kuma zambar tattalin arziƙi. Wannan ba abu ne na adalci ba ko mai kyau – yana nufin zaman ‘Amurka da tafi kowa’ da kuma ƙaruwar ƙarfin Amurka,” in ji shi.

Jakadan ya kuma yi gargadi cewa ƙasashe masu tasowa za su fi shan wahala daga wannan tsarin haraji, kuma hakan zai fi cutar da ƙasashen Afrika, ciki har da Nijeriya.

Ya bayyana cewa, “Amurka ta ɗauki mataki mara son Rai, na cewa ‘ samun ribar kasuwanci sai an yi zamba’ wanda ya kai ga kai wa ƙasashen Afrika haraji mai yawa, wanda ya saɓa wa ƙa’idojin WTO na bayar da kulawa ta musamman ga ƙasashen masu tasowa.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
  • China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji
  • ‘Yan Sandan Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara
  • Rundunar ‘Yansan Nijeriya Za Ta Gudanar Atisaye Ga Jami’anta a Jigawa
  • Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano
  • Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo
  • An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a Neja
  • Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda a Sambisa da Kudancin Tumbun