Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Saad Abubakar ya yi kira ga al’ummar Musulmin kasar nan da su fara neman ganin jinjirin watan Sha’aban a gobe Laraba 29 ga watan Janairu 2025, daidai da kalandar Musulunci 29 ga watan Rajab 1446AH.

 

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin addinin musulunci na jihar Sokoto, Farfesa Sambo Wali Junaidu, Wazirin Sokoto ya ce idan an gan shi, sai a mika bayanan ga sarki mafi kusa domin sanarda mai alfarma Sarkin Musulmi.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa, duban yana fayyace kalandar Musulunci a cikin shekara guda, wanda hakan ya zai sa ganin watan Ramadan ya fi karbuwa ga al’ummar Musulmin kasar baki daya.

 

NASIR MALALI/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wata

এছাড়াও পড়ুন:

Mayakan Kungiyar Ta’addanci Ta ISIS Sun Sake Kunno Kai A Garuruwan Deir ez-Zor Da Hasaka Na Siriya

Mayakan kungiyar ta’addanci ta ISIS sun sake kunno kai a garuruwan Deir ez-Zor da Hasaka na kasar Siriya

Yankunan Deir ez-Zor da Hasakah dake arewa maso gabashin kasar Siriya suna ci gaba da samun karuwar bullar ayyukan ta’addancin kungiyar ISIS tun daga farkon wannan wata. Hare-hare 13 sun kai sune kan Dakarun Syrian Democratic Foeces ta (SDF) ta Kurdawa masu samun goyon bayan Amurka da kuma fararen hulan yankunan, lamarin da ya janyo hasarar rayuka.

A cewar kungiyar kare hakkin bil- adama ta Syria, hare-haren sun bambanta wajen aiwatar da su, daga harin kwanton bauna zuwa na kai hari kai tsaye, wanda ke nuni da yadda kungiyar ta canza yanayin kai hare-hare a yankunan saboda matakan tsaron a garuruwan. Wadannan al’amura sun kuma nuna cewa kungiyar ta’addancin na ci gaba da yin barazana a arewaci da gabashin Siriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 
  • Demokradiyyar Kwango Ta Haramta Jam’iyyar Josept Kabila A Kasar Saboda Hulda Da Yan Tawaye
  • Ma’aikatar Lafiya Ta Yemen Ta Sanar Da Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada A Hare-Haren Amurka Kan Kasar
  • Muna Ganin Kashe-kashe Ta Ko’ina – ‘Yan Gudun Hijirar Sudan
  • Putin ya umarci tsagaita wuta a Ukraine albarkacin bikin Ista
  • An Fara Bikin Ranar Sojin A Iran 18 Ga Watan Afrilu Tare Da Gudanar da Fareti A Gaban Shugaban Kasar
  • Mayakan Kungiyar Ta’addanci Ta ISIS Sun Sake Kunno Kai A Garuruwan Deir ez-Zor Da Hasaka Na Siriya
  • Shugaban Majalisar Neja Ya Mika Sakon Easter Ga Al’ummar Kirista.
  • APC Ta Gaza Gudanar Da Taron NEC Cikin Shekaru Biyu – PDP Ta Zarge Su
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa: Makiya Suna Adawa Da Fadada Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya