An kama gungun masu yi wa Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura
Published: 28th, January 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta samu nasarar cafke gungun wasu masu yi wa mayaƙan Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura a jihohin Neja da Kaduna.
Galibai dai ’yan ta’adda a Arewacin Nijeriya sukan yi amfani da babura wajen gudanar da harkokin sufuri domin sheƙe ayarsu ta garkuwa da satar mutane da kai wa al’ummomi hare-hare.
Da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ’yan sanda da ke Abuja a ranar Talatar nan, mai magana da yawun rundunar, Benneth Igweh, ya ce sun samu nasarar ce ta hanyar bayanan sirri, inda suka cafke wasu mutum uku a Ƙaramar Hukumar Suleja ta Jihar Neja.
Igweh ya bayyana sunayen ababen zargin da ke hannu da suka haɗa da Shamsudden Yunusa mai shekara 30 da Zahraddeen Saidu mai shekara 25 sai kuma Mustapha Haruna mai shekara 22.
Ya bayyana cewa sun samu jimillar babura 22 a hannun ababen zargin da kuma tarin mukullai da wayoyin hannu.
Ya yi ƙarin haske da cewa ababen zargin sun ƙware wajen sauya fasalin babura da aka sato suna bayar da haya ko sayar wa miyagu ciki har da mayaƙan Boko Haram da suka yi sansani a jihohin Neja da Kaduna.
Ya ƙara da cewa, jagora a cikin ababen zargin—Shamsudden—ya bayyana cewa ya kan sayar da duk babur ɗaya kan farashin Naira dubu 200 zuwa 250.
“Ya faɗa mana cewa a kwanan nan ya karɓi kafin alƙalami har Naira dubu 250 a hannun wani mai suna Ibrahim Kabiru da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari domin kawo masa babura ƙirar Bajaj.
“Shi kuma Zahraddeen shi ne mai jigilar kai babu ga masu saye, inda ya shaida mana cewa ko a kwanan nan ya kai wasu babura da ya karɓo a hannun wani mai suna Mustapha a garin Suleja.
“Shi kuma Mustapha ya ƙware wajen sauya fasalin babura da yi musu gyare-gyare gabanin a sayar wa abokan hulɗarsu,” in ji Igweh.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babura Boko Haram Jihar Kaduna Jihar Neja ababen zargin
এছাড়াও পড়ুন:
Ya kashe masoyin tsohuwar matarsa bayan sakinta a Neja
Wani mutum mai suna Muhammad Ma’aba daga ƙauyen Fujeregi da ke Ƙaramar hukumar Gbako a Jihar Neja, ya mutu a hannun tsohon mijin matar da yake shirin aura.
Rahotanni sun bayyana cewa, wata Ƙungiya ƙarƙashin jagorancin tsohon mijin matar mai suna Alhaji Yikangi, daga ƙauyen Yikangi Chikan ne suka kai wa Ma’aba hari a tsakanin garin Saganuwa da Fujeregi.
PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike Benuwe: Har yanzu ba a gano wasu mutanen ƙauyuka ba – Gwamna AliaMazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, tsohon mijin ya saki matar mai suna Fatima Suleiman sau uku, amma ya dage cewa ba za ta ƙara aure ba — ko da ta samu sabon mai neman aurenta.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce, “A ranar 17/4/2025 da misalin ƙarfe 2:00 na rana, an samu labarin cewa wasu gungun mutane ƙarƙashin jagorancin wani Alhaji Yikangi na ƙauyen Chikan ta hanyar Lemu sun kai hari kan wani Muhammad Ma’aba na ƙauyen Fujeregi, dukkansu a ƙaramar hukumar Gbako.
“An samu rahoton cewa wanda aka kashe ɗin an yi masa dukan tsiya ne saboda rashin fahimtar da wata mata Fatima Suleiman da suke cikin yanki ɗaya, ya mutu a hanyar zuwa babban asibitin Lemu, inda aka tabbatar da mutuwarsa.”
Abiodun ya ƙara da cewa, ana gudanar da bincike kan lamarin, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin kamo waɗanda suka aikata wannan aika-aika.