An kama gungun masu yi wa Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura
Published: 28th, January 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta samu nasarar cafke gungun wasu masu yi wa mayaƙan Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura a jihohin Neja da Kaduna.
Galibai dai ’yan ta’adda a Arewacin Nijeriya sukan yi amfani da babura wajen gudanar da harkokin sufuri domin sheƙe ayarsu ta garkuwa da satar mutane da kai wa al’ummomi hare-hare.
Da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ’yan sanda da ke Abuja a ranar Talatar nan, mai magana da yawun rundunar, Benneth Igweh, ya ce sun samu nasarar ce ta hanyar bayanan sirri, inda suka cafke wasu mutum uku a Ƙaramar Hukumar Suleja ta Jihar Neja.
Igweh ya bayyana sunayen ababen zargin da ke hannu da suka haɗa da Shamsudden Yunusa mai shekara 30 da Zahraddeen Saidu mai shekara 25 sai kuma Mustapha Haruna mai shekara 22.
Ya bayyana cewa sun samu jimillar babura 22 a hannun ababen zargin da kuma tarin mukullai da wayoyin hannu.
Ya yi ƙarin haske da cewa ababen zargin sun ƙware wajen sauya fasalin babura da aka sato suna bayar da haya ko sayar wa miyagu ciki har da mayaƙan Boko Haram da suka yi sansani a jihohin Neja da Kaduna.
Ya ƙara da cewa, jagora a cikin ababen zargin—Shamsudden—ya bayyana cewa ya kan sayar da duk babur ɗaya kan farashin Naira dubu 200 zuwa 250.
“Ya faɗa mana cewa a kwanan nan ya karɓi kafin alƙalami har Naira dubu 250 a hannun wani mai suna Ibrahim Kabiru da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari domin kawo masa babura ƙirar Bajaj.
“Shi kuma Zahraddeen shi ne mai jigilar kai babu ga masu saye, inda ya shaida mana cewa ko a kwanan nan ya kai wasu babura da ya karɓo a hannun wani mai suna Mustapha a garin Suleja.
“Shi kuma Mustapha ya ƙware wajen sauya fasalin babura da yi musu gyare-gyare gabanin a sayar wa abokan hulɗarsu,” in ji Igweh.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babura Boko Haram Jihar Kaduna Jihar Neja ababen zargin
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Sule Ya Hori Masu Ziyarar Ibada Ta Kirista Su Zama Jakadu Na Gari
Gwamnatin Jihar Nasarawa ya hori Kiristoci masu niyyar ziyarar su zama jakadu na gari tare dayin addu’ar zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba idan sun isa can.
Gwamna Abdullahi Sule ya bayyana haka a lokacin bankwana da masu ziyarar su 162 da zasu tashi zuwa Isra’ila.
Gwamnan ya jaddada muhimmancin da’a a yayin tafiyar tasu, inda ya bayyana cewa su dauka su Allah ya nufa da wannan ziyarar a bana.
Ya kuma tabbatar wa maziyartan jihar cewa gwamnatin jihar ta himmatu wajen kyautata rayuwarsu, tare da samar da matsuguni da abinci kyauta a tsawon tafiyarsu.
Sakataren zartarwa na hukumar jin dadin hukumar kula da masu ziyarar kiristoci ta jihar Nasarawa, Davide Ayiwa, wanda ya yabawa gwamnatin jihar kan gyaran ofishin hukumar ya kuma bukaci maziyartan da su ci gaba da gudanar da aikinsu.
Bikin ya samu halartar mataimakin gwamnan jihar Dr. Emmanuel Akabe da alkalin alkalan jihar, Mai shari’a Aisha Bashir Aliyu, kwamishiniyar yada labarai da sauran kwamishinoni da sakataren gwamnatin jihar Labaran Shu’iabu Magaji babban akanta janar na jihar.
COV/Aliyu Muraki/Lafia