Ya gargaɗi kamfanonin da suka samu kwangilar da su tabbatar da ingantaccen aiki, tare da jaddada cewa za a hukunta duk wanda ya kasa cika sharuɗan aikin.

Sannan, ya buƙaci direbobin manyan motoci da su guji lodin da ya fi ƙarfin titin domin kare lafiyar matafiya da rage hatsari.

Don haka, gwamnati za ta kafa kwamiti don tabbatar da bin doka da oda a kan titin.

Kwamishinan ayyuka na jihar, Injiniya Abdullahi Umar Faruk, ya bayyana cewa kashi 40 na kuɗin aikin an riga an biya.

Ya ce an biya kamfanonin kuɗin kamar haka:

Kamfanin ZBBC zai shimfiɗa titin daga Dabai zuwa Mahuta (kilomita 25) a kan Naira biliyan 18. Kamfanin Habib Engineering LTD zai yi aikin daga Mahuta zuwa Marafa (kilomita 25) a kan Naira biliyan 18. Kamfanin GNIC zai yi aikin daga Koko zuwa Marafa (kilomita 37) a kan Naira biliyan 27.

Baya ga titin Koko – Zuru, Gwamna Idris ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar za ta inganta babban asibitin Zuru domin ya zama cibiyar ƙwararru.

Haka nan, a yayin ziyarar godiya da ya kai ƙananan hukumomin Fakai, Sakaba, Danko Wasagu, da Zuru, ya kuma ƙaddamar da wata hanyar karkara mai tsawon kilomita 11 daga Koko zuwa garin Kangin Korama, wanda aikin zai ci Naira biliyan 1.3.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Nasir kan Naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya bayyana cewa: Babban abin da suke bukata a duk wata tattaunawa shi ne a dage takunkumi

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Isma’il Baqa’i, ya jaddada cewa babban bukatar Iran a duk wata tattaunawa ita ce a dage takunkumin da aka kakaba mata ta hanyar da za ta kai ga samun sakamako mai ma’ana.

Isma’il Baqa’i ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai na mako-mako da yake yi a yau litinin cewa: A kwanakin baya ministan harkokin wajen kasar Iran ya ziyarci kasar Rasha, sannan ya gana da ministan harkokin wajen kasar Italiya, a gefen shawarwari ba na kai tsaye ba tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Amurka.

Ya kara da cewa: A gobe ne ministan harkokin wajen kasar Iran zai kai ziyarar aiki zuwa kasar China. Ya kuma kara da cewa, ana ci gaba da samun wasu ci gaba a daidai wadannan ziyarce-ziyarcen, yana mai jaddada cewa idan aka yi tambayoyi a kansu a yayin taron tambayoyi da amsa, zai ba da cikakkun bayanai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Darajar Cinikin Sarin Kaya Da Sayen Kayan Masarufin Sin Ta Karu Da Dala Biliyan 452.5 a Rubu’In Farkon Bana
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • Yadda ma’aikatan gidan ruwa 4 suka mutu a Bauchi
  • KOFIN DUNIYA: Za A Kara Yawan Kasashen Da Suke Bugawa Zuwa 64 A Shekarar 2030
  • Shin Mataimakin Gwamnan Bauchi ya ‘mari’ Ministan Tinubu?
  • Shin Ziyarar Bazata Zuwa Gidan Budurwa Daga Saurayi Na Bata Wa ‘Yanmatan Rai?
  • ’Yan sanda sun ceto ɗalibai 10 sun kashe ɗan bindiga a Edo
  • ’Yan sanda sun ceto ɗalibai 10 sun lashe ɗan bindiga a Edo
  • Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare
  • Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97