Aminiya:
2025-04-23@02:26:06 GMT

An dakatar da Max Air na tsawon wata 3 bayan hatsari a Kano

Published: 29th, January 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya, ta dakatar da zirga-zirgar jiragen Max Air na tsawon wata uku, bayan ɗaya daga cikin jiragen kamfanin, tayarsa ta yi bindiga yayin sauka a filin jirgin saman Malam Aminu Kano a daren ranar Talata.

Jirgin Max Air ƙirar Boeing 734 mai lamba 5N-MBD ne ya samu matsalar kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Za a dawo da ’yan Najeriya sama da 5,000 da ke zaune a Amurka Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici

Dukkanin fasinjoji 53 da ke cikin jirgin sun kuɓuta cikin ƙoshin lafiya.

Wannan shi ne karo na uku da jirgin Max Air ke fuskantar matsala cikin watanni uku da suka gabata.

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Ƙasa (NCAA), ta sanar da dakatarwar domin bai wa kamfanin damar sake duba yanayin aikinsa, yayin da Hukumar Binciken Haɗuran Jiragen Sama (NSIB), ta fara bincike kan lamarin.

Daraktan Harkokin Jama’a da Kare Haƙƙin Fasinjoji na NCAA, Michael Achimugu, ya yi ƙarin haske kan lamarin.

Ya ce, “Za mu iya gano musababbin wannan hatsari ne kawai bayan binciken NSIB, amma dole ne mu ɗauki matakan kariya don tabbatar da tsaro.”

Ya ƙara da cewa, “A lokacin dakatarwar watanni uku, NCAA za ta gudanar da cikakken bincike kan tsaro da kuma ƙarfin tattalin arziƙin Max Air.

­“Kamfanin jirgin zai iya ci gaba da zirga-zirga ne kawai idan ya cika dukkanin sharuɗan da ake buƙata.”

NCAA ta nemi afuwar fasinjojin da wannan mataki zai shafa, amma ta jaddada cewa lafiyar fasinjoji ita ce abin da yafi muhimmanci a wajenta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ababen fashewa dakatarwa fashewa Hatsari Jiragen sama Taya

এছাড়াও পড়ুন:

Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, sharhin bayan labarammu na yau za yi magana dangane da “Rage kisasfin kudan ma’aikatar harkokin wajen Amurla da kimani kasha 50% da kuma tasirinsa ga matsayin Amurka a duniya da kuma cikin gida. Wanda ni tahir amin zan karanta.

A makon da ya gabata ne shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bada sanarwan, rahe kasafin kudi na ma’aikatar harkokin wajen kasar da kasha 50%, saboda haka kuma ya rufe wasu daga cikin ofisoshin jakadancin kasar da kananan ofisoshin jakadancin kasar fiye da 30 a yankuna daban daban a duniya amma mafi yawansu a nahiyar Afirka.

Dangane da wannan matakin da gwamnatin kasar Amurka masana daga ciki ga wajen kasar ta Amurka masu yawa sun nuna damuwarsu da kuma rashin amincewarsu da hakan.

A majalisar dokokin kasar, wakilai daga jam’iyyu biyu masu mulkin Amurka wato Republican da kuma Democrat sun nuna rashin amincewarsu da matakan da shugaba Trump ya dauka, suna kuma ganin hakan wata alama ce jada bayan Amurka daga harkokin kasashen duniya, kuma da haka tauraron kasar zata dushe a duniya. Sannan akwai has ashen cewa kasar China zata maye gurbin Amurka a cikin al-amura da dama, musamman a kasashen da Amurka ta janye.

Kafin haka dai shugaban kasar Amurka ya janye kasar Amurka daga manya-manayn kungiyoyin bada agaji a duniya, wadanda suka hada da hukumar lafiya ta duniya WHO, hukumar abinci ta duniya.

Banda haka Amurka ta janye tallafin da take bawa kungiyar tsaro ta NATO wanda yake taimakawa abokan kasar na turai kan abubuwan da suka shafi tsaro, da kuma wasu al-amur da dama.

Masu sukan shugaban daga cikin har da sanatoci da tsoffin janar-janar na sojojin Amurla wadanda suka yi ritaya kimani 120 suke ganin, shugaban trump ya mikawa kasashen China da rasha dukkan wuraren da ya janye tallafi, ko kuma ya rufe ofishin jakadancin Amurka a duniya.

Wadannan masana dai suna ganin, ragewa ma’aikatar harkokin wajen kasar kudede masu yawa wanda ya kai dalar biliyon kimani 25, ya nuna cewa gwamnatin Amurka bata da wakilai a wasu wurare masu mihimmanci da dama a duniya, don haka ba zata sami labarin abinda yake faruwa a cikinsu ba. Kuma mai yuwa samun wadannan labarai suna da muhimmanci.

Wasu masu sukan suna ganin a halin da ake ciki mafi yawan kawayen Amurka, musamman kasashen turai sun tashi daga abokan aiki zuwa ga makiya ga gwamnatin Amurka. Sannan a kasashen masu tasowa, wadanda suke neman tallafi da taimako, Amurka ta bawa kasar China da Rasha dama ta su amfana da wadannan kasashe, ko basu bada kyauta ba, amma suna iya zuba jari a cikin kasashen inda bangarorin biyu zasu amfana.

A wani bangare kuma shugaban yana da shirin rage kudaden da ake kashewa ayyukan gwamnati a cikin gida, inda hakan ya kai ga rufe kafafen yada labarai da daman a gwamnatin Amurka. Hakan ya sa mutane da dama sun rasa ayyukansu a cikin kasar. Sannan daga kasashen waje ba, dubban ma’aikata sun rasa ayyukan daga kungiyoyin bada agaji ko kiwon lafiya ko tallafawa yara karkashin MDD wadanda gwamnatin Trump ta janye tallafin da suke bayarwa.

Daga karshe masana suna ganin, idan wannan halin ya ci gaba da alamun shugaba Donal Trump kama hanyar rusa kasar Amurka daga ciki da kuma wajen kasar a cikin shekaru 4 da zai yi a matsayin shugaban kasa. Mai yuwa gwamnatin da zata zo bayan tasa ta gaggauta gyaran wasu daga cikin abubuwan da ya bata. Amma wasu barnan da yayi ba zasu sake gyaruwa ba.

Don haka daga karshen dai Amurka ta kama hanyar wargajewa, idan ba an yi wani abu da gaggawa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • Gwamna ya dakatar da basarake kan satar mutane da yankinsa
  • Tinubu Ya Komo Nijeriya Bayan Ziyarar Mako 3 A Turai
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Hisbah A Katsina Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Wata Budurwa A Wani Faifan Bidiyo
  • Leicester City Ta Koma Gasar Yan Dagaji Bayan Shan Kashi A Hannun Liverpool
  • Sharhi:  Kalankuwar  Kona Rayayyu Da Wuta A Gaza
  • Faransa : An kama wata ‘yar Iran mai goyon bayan Falasdinu
  • Kasar Rasha Ta Sanar Da Tsagaita Bude Wuta Da Ukraine Na Tsawon Kwanaki Bikin Ester