Aminiya:
2025-04-02@17:31:39 GMT

An dakatar da Max Air na tsawon wata 3 bayan hatsari a Kano

Published: 29th, January 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya, ta dakatar da zirga-zirgar jiragen Max Air na tsawon wata uku, bayan ɗaya daga cikin jiragen kamfanin, tayarsa ta yi bindiga yayin sauka a filin jirgin saman Malam Aminu Kano a daren ranar Talata.

Jirgin Max Air ƙirar Boeing 734 mai lamba 5N-MBD ne ya samu matsalar kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Za a dawo da ’yan Najeriya sama da 5,000 da ke zaune a Amurka Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici

Dukkanin fasinjoji 53 da ke cikin jirgin sun kuɓuta cikin ƙoshin lafiya.

Wannan shi ne karo na uku da jirgin Max Air ke fuskantar matsala cikin watanni uku da suka gabata.

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Ƙasa (NCAA), ta sanar da dakatarwar domin bai wa kamfanin damar sake duba yanayin aikinsa, yayin da Hukumar Binciken Haɗuran Jiragen Sama (NSIB), ta fara bincike kan lamarin.

Daraktan Harkokin Jama’a da Kare Haƙƙin Fasinjoji na NCAA, Michael Achimugu, ya yi ƙarin haske kan lamarin.

Ya ce, “Za mu iya gano musababbin wannan hatsari ne kawai bayan binciken NSIB, amma dole ne mu ɗauki matakan kariya don tabbatar da tsaro.”

Ya ƙara da cewa, “A lokacin dakatarwar watanni uku, NCAA za ta gudanar da cikakken bincike kan tsaro da kuma ƙarfin tattalin arziƙin Max Air.

­“Kamfanin jirgin zai iya ci gaba da zirga-zirga ne kawai idan ya cika dukkanin sharuɗan da ake buƙata.”

NCAA ta nemi afuwar fasinjojin da wannan mataki zai shafa, amma ta jaddada cewa lafiyar fasinjoji ita ce abin da yafi muhimmanci a wajenta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ababen fashewa dakatarwa fashewa Hatsari Jiragen sama Taya

এছাড়াও পড়ুন:

Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya

A Bikin Yawan Sallah na Jafi da aka yi a fadar Sarkin Gombe, Mai Martaba Alhaji Abubakar Shehu Abubakar III, ya yi kira ga manoma da makiyaya da su zauna lafiya da juna.

Sarkin ya ce zaman lafiya shi ne ginshiƙin ci gaba, kuma haɗin kai tsakanin manoma da makiyaya zai hana rikice-rikice da ke barazana ga jihar.

Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano Gwarzon gasar Alƙur’ani ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga a Katsina

“Ina roƙon manoma da makiyaya da su zauna lafiya don guje wa rigingimu.

“Kowa yana da haƙƙin tabbatar da zaman lafiya domin hakan na kawo ci gaban tattalin arziƙi da walwalar al’umma,” in ji Sarkin.

Haka kuma, ya tabbatar da cewa masarautar Gombe za ta ci gaba da goyon bayan gwamnatin jihar domin tabbatar da tsaro mai ɗorewa.

Sarkin ya gode wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa ƙoƙarinsa na inganta rayuwar al’umma da ɗaukar matakan tsaro, musamman samar da motocin aiki ga jami’an tsaro.

Bikin hawan sallah na Jafi ya samu halartar manyan baƙi, ciki har da Gwamnan Jihar Gombe da wasu manyan jami’an gwamnati, inda aka jaddada buƙatar haɗin kai da zaman lafiya a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Galadiman Kano, Abbas Sanusi
  • Mutum 2 sun rasu, 13 sun ɓace a hatsarin jirgin ruwa a Bayelsa
  • Sojojin Yemen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kataparen Jirgin Ruwan Yaki Mai Daukar Jirage Na kasar Amurka
  • Sojojin Yemen Sun Harbo Jirgin Leken Asirin Amurka Samfurin MQ9
  • Ta zuba wa abokan aikinta guba bayan taƙaddama kan ƙarin matsayi
  • Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF
  • Faransa : An haramta wa Marie Le Pen, takara har tsawon shekaru 5
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya
  • Sarkin Gombe ya nemi manoma da makiyaya su zauna lafiya
  • Mutane 9 Sun Mutu Sanadin Haɗarin Mota A Katsina