Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da rashin amincewar kasashen masar da Jordan kan maida Falasdnawa cikin kasashensu wanda ni tahir amin zan karanta.

A makon da ya gabata ne shugaban kasar Amurka Donal Trump ya fadawa kafafen yada labarai a lokacinda yake cikin jirgin fadar shugaban kasa ko ‘Air Force 1, kan cewa yana duba yiyuwar kwasar Falasnidawa a Gaza zuwa kasar Masar sannan sauran falasdinawa a yankin yamma da kogin Jordan da kuma sauran wurare a kasar Falasdinu da aka mamaye zuwa kasar Jordan.

Wannan zancen dai ba sabuwa bace, a rikicin gabas ta tsakiya, shuwagabanin Amurka a baya, sun yi wannan maganar amma bata yuba.

A halin yanzun babu wata kasa, ya zuwa yanzu a duniya, wacce take goyon bayan ra’ayin shugaba Trump a kan wannan tunanin.

Shugaban kasar Masar Abdulfattah Assisi a wani jawabin da ya gabatar ya bayyana cewa kasarsa ba zata taba amincewa da kaurar Falasdinawa zuwa kasarsa ba, don yin haka zalunci ne a fili, banda haka hatsari ne ga kasar masar kanta.

Gwamnatin kasar Jordan ma ta ki amincewa da hakan, banda haka rikicin gabas ta tsakiya ta zama rikici ne wanda yake girgiza dangantaka tsakanin kasashen yankin da ma, tsakanin sauran kasashen duniya. Har iyala yau rikicin zai tama dokokin kasa da kasa kan al-amura da dama. Daga cikin har da dokokin kasa da kasa, wadanda suka yi magana dangane da yencin zama dan wata kasa, da kuma yadda kasashen duniya suke daukar mutane a tsakaninsu.

A halin yanzu miliyoyin Falasdinawa suna rayuwa a kasashen Jordan, Siriya da Lebanon da Masar, da ma wasu kasashe a duniya. Wadannan a saryar da hakkinsu na komawa kasarsu ta asali, a inda ba’a dauke su yan kasa ba. Suna rayuwa a sansanonin yan gudun hijira fiye da shekaru 76. Akwai wata al-umma wacce aka zalunta a doron kasa kamar Falasdinawa?.

Banda haka maida Falasdinawa zuwa kasashen Masar da Jordan, don tabbatarwa yahudawan sahyoniyya kasar Falasdinu, zai tabbatar da rashin adalcin gwamnatin Amurlka a fili. Duk da cewa tana ci gaba da zaluntar Falasniya tun da dadewa ta bayan fage sannan a zahri wasu lokuta. Sai dai a wannan fagen kowa a duniya sai ya fahinci hakan.

Banda haka wannan zai jawa matsalar yan gudun hijira a kasashe daban daban na duniya, misali yan gudun hijira na Rohinga, sai a ce dole su koma kasar Bagladesh don su musulmi ne, alhali su yan kasar Myanmar ne, al’adarsyu ta mutanen myan marne kuma harshensu harshen myan mar ne.

Daon haka wannan ra’ayin idan ya tabbata zai rikita al-amuran zamantakewa a kasashen duniya da dama, musamman inda ake da yan gudun hijira.

Shugaban Assisi a jawabinsa ya bayyana cewa, gwamnatin kasarsa tana ganin hanyar warware wannan matsalar itace samar da kasashe biyu a kasar Falasdinu, kuma zata taimaka don tabbatar da hakan.

Kasashen larabawa gaba daya, tun da dadewa sun fitar da batun zaman Falasdnbiawa a wasu kasashen larabawa ko kuma wani wuri daban, suna ganin dole ne a maidasu kasaru ko ba dade ko ba jima.

Sai dai dangane da samar da kasashe biyu wanda wasu kasashen larabawa suke ganin cewa itace hanya tilo wajen warware wannan matsalan. Da farko su yahudawan da suka mamaye kasar Falasdinu shekaru fiye da 70 da suka gabata basu amince da haka ba, banda haka suna ma neman kara kwace wasu kasashen larabawa makobta da su don kara yawan kasar da suka mamaye. Sannan Falasdinawa masu asalin kasa basu amince da haka. Sun ganin kasar Falasdinu ta Falasdinawa ne daga tekun medeteranin har zuwa gogin Jordan.

Don haka idan har wadanda ake magana a kansu gaba daya basu amince da haka ba, to ra’ayin samar da kasashen biyu a kan kasar Falasdinu da aka mamaye ma, tilastawa mutanen biyu abinda ba ra’ayinsu bane.

Yanzu dai sai mu jira mu gani abinda Trump zai yi don tabbatar da ra’ayinsa.

Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen larabawa yan gudun hijira kasar Falasdinu wasu kasashe

এছাড়াও পড়ুন:

Babban daraktan hukumar IAEA, Rafael Grossi, zai ziyarci Iran cikin makwanni masu zuwa

Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa Rafael Grossi ya sanar da shirin kai ziyara birnin Tehran nan da makwanni masu zuwa a yayin da ake ci gaba da tattaunawa don tsaida takamaimen lokacin.

Ziyarar ta zo ne a wani bangare na ci gaba da huldar diflomasiyya tsakanin Iran da hukumar IAEA, da nufin tinkarar batutuwan da suka shafi Nukiliya, da samar da hadin gwiwar fasaha cikin tsarin alkawurran da Iran ta dauka a karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT).

Ziyarar ta kuma jaddada irin hadin gwiwar da Tehran ke ci gaba da yi da hukumar ta IAEA, duk da matsin lamba daga waje da kuma zargin siyasa daga kasashen yammacin Turai.

Da yake amsa tambaya daga wakilin TASS, Grossi ya tabbatar da cewa ana tattaunawa don tsara ziyararsa a makonni masu zuwa.

Wannan bai ta ce ziyarar Rafael Grossi, t afarko a Iran ba, don kuwa ko a kasrhen  watan Nuwamban bara ya gana da shugaban Iran Masoud Pezeshkian da ziyarce-ziyarcen cibiyoyin nukiliya na Fordow da Natanz.

Ziyarar Grossi ta zo ne a daidai lokacin da Iran ke ci gaba da tabbatar da hakkinta na samar da makamashin nukiliya cikin lumana karkashin dokokin kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban daraktan hukumar IAEA, Rafael Grossi, zai ziyarci Iran cikin makwanni masu zuwa
  • Isra’ila na karbe yankuna a zirin Gaza
  • Yadda Sabon Tsarin Harajin Kwastam Na Amurka Ke Shirin Gurgunta Tsarin Kasuwanci Na Duniya
  • Iran Ta Bukaci Hukumar IAEA Ta Bayyana Matsayinta A Shirin Makamashin Nukliya Na Kasar
  • Wang Yi Ya Jinjina Wa Gudummawar Da Sinawa Da ’Yan Rasha Suka Bayar A Yakin Duniya Na Biyu
  • Kasar Sin Mai Tabbatar Da Daidaito A Duniya Mai Cike Da Rashin Tabbas
  • Kungiyar RED CROSS Ta Duniya Ta Yi Allawadai Da HKI Saboda Kissan Likitoci 8 A Asbitin Rafah
  • NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Komawa Cin Abinci Yadda Ya Kamata Bayan Watan Ramadana
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Kasashen Yamma Sune Yan Ta’adda Na Gasliya A Yankin
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya