Shugaba Felix Tshisekedi na Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo, ya bayyana cewa sojojin ƙasar na tunkarar ’yan tawayen M23 da suka kaɗɗammar da munanan hare-hare tare da ƙwace ikon muhimman wurare a Birnin Goma da ke gabashin ƙasar.

Hare-haren mayaƙan M23 da ke samun goyon bayan ƙasar Rwanda sun kashe Gwamnan Birnin Goma, a makon jiya a yayin da dubban mutane ke gudun hijira domin tsira da rayukansu.

A ranar Laraba mayaƙan M23 suka ƙwace wasu yankuna biyu a Lardin Kivu da ke gabashin ƙasar, daga hannun sojoji.

A jawabinsa na ranar Laraba ta talabijin, Shugaba Tshisekedi ya zargi ƙasashen duniya kan rashin ɗaukar mataki kan lamarin, musamman hannun Rwanda a cikin lamarin, wanda ya ce katsalandan ne ga dimokuraɗiyya kuma yana iya ƙara munin al’amarin.

NAJERIYA A YAU: Ainihin Dalilan Taƙaddama Kan Kafa Kotunan Musulunci A Kudu Za a dawo da ’yan Najeriya sama da 5,000 da ke zaune a Amurka

Ƙazancewar halin da ke ciki a Gabashin kasar ta DR Congo ya haifar da fargabar ƙara taɓarɓarewar yanayin rayuwar ’yan gudun da matsalar abubuwan more rayuwa a ƙasar.

Amma a ranar Laraba Shugaba Tshisekedi ya bayyana cewa ’yan tawayen suna ɗanɗana kuɗarsu a hannun sojojin ƙasar mai arziƙin zinare da lu’ulu da sauran ma’adinai.

Shugaba Felix Tshisekedi, a jawabinsa na farko tun bayan faruwar hare-haren na M23 a tsawon makonni, ya bayyana cewa sojojin sun samu gagarumar nasara.

Gabashin ƙasar Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo ya shafe shekaru sama da 30 yana fama rikici inda ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai ke addabar al’umma, baya ga tawaye ga gwamnati.

Ana alaƙanta wanna rikici da kisan kiyashi da aya auku a shekarar 1994 lokacin yaƙin basasa ƙasar Rwanda, maƙwabciyar DR Congo.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mayaƙan M23 Rwanda

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara

Dakarun Sojin ‘Operation FANSAN YANMA’, sun kama Ƙasurgumin Shugaban ’Yan Bindiga, Kachallah Hassan Nabamamu, wanda ya addabi al’ummar Mada, Tsafe, da wasu yankunan Jihar Zamfara.

Dakarun sun kai farmaki Hegin Mahe, Ruwan Bore, garin Mada, a Ƙaramar Hukumar Gusau a ranar 27 ga watan Fabrairu.

Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa Rage Albashi: Abba ya dakatar da muƙaddashin shugaban ma’aikatan Kano

Bayan musayar wuta, sojoji sun kashe wasu ’yan bindiga, yayin da Nabamamu ya tsere zuwa cikin wani gida, amma daga ƙarshe dakarun suka cafke shi.

Bayan kama shi, ɗaya daga cikin yaransa, Bakin Malam, ya jagoranci kai harin ramuwar gayya wasu ƙauyuka, wanda ya tilasta wa mazauna ƙauyukan tserewa.

Sai dai dakarun sun mayar da martani, inda suka fatattaki ’yan bindigar, tare da ƙara jibge sojoji don tabbatar da tsaro a yankin.

Nabamamu, ya kasance almajiri ne, daga baya ya zama hatsabibin ɗan bindiga wanda ya yi sanadin ajalin mutane masu yawan gaske.

Ya jagoranci sama da mayaƙa 100, inda yake karɓar haraji daga hannun mazauna wasu ƙauyuka, kuma yana da alaƙa da masu yi wa wasu mahara safarar makamai a yankin.

Kama shi na iya rage ƙarfin ’yan bindiga a Zamfara, yayin da sojoji ke ƙara ƙaimi domin kawar da barazanar tsaro da tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda za ku yi rajista a shafin Itikafi a Saudiyya
  • Saudiyya ta buɗe shafin rajistar masu Itikafi
  • Ramadan: Hon Jaji Ya Ƙaddamar Da Tallafin Abinci Ga Mutane Sama Da 500,000 A Zamfara
  • Sojoji sun ƙwato makamai a dajin Sambisa
  • Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida
  • Zelensky : Ban Ga Laifin Da Na Yi Wa Trump, Ballantana In Nemi Afuwa
  • MDD Ta Bayyana Cewa Yara Fiye Da 100,000 Ne Suka Ka Yi Rijistan Fara Karatu A Makarantun Gaza Na Sabuwar Shekarar Karatu
  • Sojoji sun kama shugaban ’yan bindiga, Kachallah Nabamamu a Zamfara
  • An ga jinjirin watan Ramadan a Saudiyya 
  • Cibiyar bincike ta nemi a tabbatar da dokar kare haƙƙin mata a Arewa