Tubabbun ’yan Boko Haram 5,000 sun koma cikin jama’a
Published: 31st, January 2025 GMT
Mayaƙan Boko Haram aƙalla 5,000 da suka tuba sun koma cikin al’umma da iyalansu, a cewar Cibiyar Yaƙi da Ta’addabnci na Ƙasa.
Cibiyar, wadda ke ƙarƙashin Ofishin Mashawarcin Shugaban Ƙasa Kan Sha’ani Tsaro ta bayyana cewa babu ko mutum ɗaya da cikin tubabbun mayaƙan na Boko Haram da ya sake ɗaukar makami.
Ta bayyana cewa gwamnatin Jihar Borno ta tabbatar cewa wata shida bayan kammala ba su horo da sauya tunanin tsofaffin mayaƙan, amma har yanzu babu labarin ko mutum ɗaya daga cikinsu da ya yi tubar muzuru.
Shugabar Sashen Daƙile Rikice-rikice Masu Alaƙa da Tsattsauran Ra’ayi (PVEA) ta Cibiyar, Ambasada Mairo Musa Abbas, ce ta bayyana haka a yayin taron gwamnonin yankin Tafkin Chadi a Maiduguri, Jihar Borno.
NAJERIYA A YAU: Anya Jam’iyyar PDP Za Ta Kai Labari A Fagen Siyasar Najeriya Kuwa? KAROTA za ta kashe N250m wajen gyaran motoci 5 a Kano Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-RufaiDa take jawabi kan kula da masu ficewa daga Boko Haram da kuma kawo ƙarshen kungiyoyi masu ɗaukar makamai, Ambasada Mairo ta jaddada muhimmancin amfanin da matakai da dabaru na bai-ɗaya a tsakanin gwamnonin ya kin domin magance matsalar tsaron.
Ta ce shirin Operation Safe Corridor da ke karɓa ta tare da sauya tunanin tubabbun ’yan Boko Haram ya yi nasarar sauya tunanin tsofaffin mayaƙan ƙungiyar guda 5,000.
A cewarta, Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) tana aiki da sarakunan gargajiya da malaman addini a duk ƙananan hukumomi 774 da ke faɗin ƙasar nan domin sanya ido kan yanayin rayuwar tubabbun mayaƙan da suka dawo cikin al’umma.
Ta kuma jinjina wa tsarin da Gwamnatin Jihar Borno ta jagoranta kan tubabbun mayaƙan da masu tsattsauran ra’ayi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Mayaƙan Boko Haram
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Shirya Taron Bita Don Jami’an Watsa Labarai
Gwamnatin jihar Kano tare da hadin gwiwar Cibiyar Hulda da Jama’a ta Najeriya (NIPR) sun shirya taron karawa juna sani na tsawon kwanaki uku ga jami’an yada labarai.
Taron na da nufin baiwa Jami’an Watsa Labarai dabarun sadarwa na zamani, tare da mai da hankali kan sabbin hanyoyin inganta sadarwar jama’a a zamani.
Da yake bayyana bude taron, kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya jaddada kudirin gwamnati na ganin sun kware a fannin sadarwa.
Ya jaddada mahimmancin kayan aikin zamani,tare da haɗin gwiwar kafofin watsa labarun, da sadarwa ta hanyar bayanai don tabbatar da ingantaccen kuma da yada bayanai akan lokaci.
Ya kuma bayyana muhimmiyar rawar da Jami’an Watsa Labarai ke takawa wajen tsara fahimtar jama’a, tabbatar da gaskiya, da kuma kiyaye amanar jama’a.
Kwamishinan ya yabawa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa amincewa da bayar da tallafin da bayar da horon, inda ya bayyana cewa gwamnati ta bada fifiko wajen bunkasa dan adam a matsayin ginshikin gudanar da shugabanci na gari.
Babban sakataren ma’aikatar, Adamu Bala Muhammad, ya ja hankalin mahalarta taron da su kara yawan wannan dama da kuma amfani da ilimin da suka samu wajen inganta sadarwa da bayar da hidima ga gwamnati.
Shugaban Hukumar NIPR na Jihar Kano, Aliyu Yusuf, ya yabawa gwamnatin jihar bisa daukar nauyin gudanar da taron bitar tare da amincewa da yin rajistar duk jami’an yada labarai na NIPR.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, taron ya kunshi kwararrun masu gudanarwa daga hukumar NIPR, wadanda za su karfafa wa mahalarta taron su kara kaimi da dabarun gudanar da ayyukansu.
KHADIJAH ALIYU