Aminiya:
2025-04-05@12:12:57 GMT

Tubabbun ’yan Boko Haram 5,000 sun koma cikin jama’a

Published: 31st, January 2025 GMT

Mayaƙan Boko Haram aƙalla 5,000 da suka tuba sun koma cikin al’umma da iyalansu, a cewar Cibiyar Yaƙi da Ta’addabnci na Ƙasa.

Cibiyar, wadda ke ƙarƙashin Ofishin Mashawarcin Shugaban Ƙasa Kan Sha’ani Tsaro ta bayyana cewa babu ko mutum ɗaya da cikin tubabbun mayaƙan na Boko Haram da ya sake ɗaukar makami.

Ta bayyana cewa gwamnatin Jihar Borno ta tabbatar cewa wata shida bayan kammala ba su horo da sauya tunanin tsofaffin mayaƙan, amma har yanzu babu labarin ko mutum ɗaya daga cikinsu da ya yi tubar muzuru.

Shugabar Sashen Daƙile Rikice-rikice Masu Alaƙa da Tsattsauran Ra’ayi (PVEA)  ta Cibiyar, Ambasada Mairo Musa Abbas, ce ta bayyana haka a yayin taron gwamnonin yankin Tafkin Chadi a Maiduguri, Jihar Borno.

NAJERIYA A YAU: Anya Jam’iyyar PDP Za Ta Kai Labari A Fagen Siyasar Najeriya Kuwa? KAROTA za ta kashe N250m wajen gyaran motoci 5 a Kano Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai

Da take jawabi kan kula da masu ficewa daga Boko Haram da kuma  kawo ƙarshen kungiyoyi masu ɗaukar makamai, Ambasada Mairo ta jaddada muhimmancin amfanin da matakai da dabaru na bai-ɗaya a tsakanin gwamnonin ya kin domin magance matsalar tsaron.

Ta ce shirin Operation Safe Corridor da ke karɓa ta tare da sauya tunanin tubabbun ’yan Boko Haram ya yi nasarar sauya tunanin tsofaffin mayaƙan ƙungiyar guda 5,000.

A cewarta, Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) tana aiki da sarakunan gargajiya da malaman addini a duk ƙananan hukumomi 774 da ke faɗin ƙasar nan domin sanya ido kan yanayin rayuwar tubabbun mayaƙan da suka dawo cikin al’umma.

Ta kuma jinjina wa tsarin da Gwamnatin Jihar Borno ta jagoranta kan tubabbun mayaƙan da masu tsattsauran ra’ayi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Mayaƙan Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗalibai za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano, ta bayyana cewa ɗaliban makarantun kwana na gwamnati da na masu zaman kansu za su koma makaranta a ranar Lahadi 6 ga watan Afrilu, 2025.

Wannan ya shafi makarantun firamare da sakandare domin ci gaba da zangon karatu na uku na shekarar 2024 zuwa 2025.

Boko Haram haram ta kashe ɗan sanda a sabon hari a Borno An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labarai

Ga ɗaliban makarantun jeka ka dawo kuwa, za su koma makaranta a ranar Litinin 7 ga wata. Afrilu, 2025.

Sanarwar da Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, ya fitar, ta buƙaci iyaye da su kula da wannan rana domin tabbatar da cewa yara sun koma makaranta a kan lokaci.

Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dokta Ali Haruna Makoda, ya gargadi ɗalibai da su guji kawo miyagun abubuwa kamar wuƙa, reza ko ƙwayoyi zuwa makaranta.

Ya kuma ce gwamnati za ta ɗauki mataki a kan duk ɗalibin da ya ƙi bin wannan doka.

Ya ƙara da cewa bin doka da ƙa’ida na taimaka wa ɗalibai su samu nasara a karatunsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗalibai za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnatin Kano
  • Ɗaliban Kano za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnati
  • Boko Haram haram ta kashe ɗan sanda a sabon hari a Borno
  • ’Yan sanda ku yi amfani da iko cikin adalci — CP Wakili
  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Matakan Harajin Fito Na Amurka Sun Sa Ta Zama Makiyiyar Duniya
  • Boko Haram: An kashe ɗan sanda a sabon hari a Borno
  • Dubban Jama’a Sun Sallaci Gawar Sheikh Idris Dutsen Tanshi
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta miƙa Janar Tsiga da wasu ga NSA
  • Najeriya ta yi kuskuren barin Boko Haram ta yi ƙarfi — Muftwang
  • Mutum ɗaya ya rasu, 3 sun jikkata a rikicin ’yan sara-suka a Filato