Idris ya ce: “Waɗannan bala’o’i ne da yawancin su ɗan’adam ke haddasawa, kuma ba za mu bari su ci gaba da faruwa ba.

 

“Shugaban Ƙasa ya umarci Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) da ta ƙara ƙaimi wajen faɗakar da jama’a da wayar da kan ‘yan Nijeriya, musamman masu wannan haramtacciyar sana’a. Wannan yanki yana da albarkatun ma’adinai da dama.

 

“Kwanan nan, Ma’aikatar Raya Ma’adinai ta Tarayya ta fara gyaran tsarin haƙar ma’adinai a faɗin ƙasar nan, kuma muna fatan za su ɗauki wannan darasi da muhimmanci.”

 

Ministan ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarni ga Ma’aikatar Raya Ma’adanai ta Tarayya da ta ƙara ƙaimi wajen tsaftace harkar haƙar ma’adanai don kauce wa irin waɗannan haɗurran.

 

Haka kuma, ministan ya jaddada damuwar Shugaban Ƙasa kan yawaitar irin waɗannan bala’o’i a faɗin ƙasar nan, yana mai cewa dole ne a ƙara wayar da kan al’umma domin daƙile aukuwar irin su a nan gaba.

 

Ya ce: “Abu na farko da ya kamata mu gane shi ne irin wannan bala’i yana faruwa sau da yawa a ƙasar mu, kuma Shugaban Ƙasa yana cikin matsanancin baƙin ciki. Ya kuma umarta cewa Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa ta gudanar da wayar da kai da faɗakarwa, musamman a cikin waɗannan ƙauyuka, domin hana aukuwar irin hakan a nan gaba.”

 

A ƙarshe, Idris ya yaba da ƙoƙarin da gwamnatin Jihar Neja ta yi wajen ɗaukar matakin gaggawa game da lamarin, tare da bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta umarci Ma’aikatar Harkokin Jin Ƙai da Rage Talauci tare da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da su taimaka wa waɗanda abin ya shafa.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Shugaban Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar

“Mun zo nan ne a madadin gwamnatin tarayya domin ganowa da kuma jajanta muku rashin da aka yi, muna so mu tabbatar muku da cewa jami’an tsaro za su kawo karshen wannan kashe-kashen na rashin hankali.

 

“An yi mini cikakken bayani, kuma ina so in tabbatar muku cewa mun fahimci tushen wannan batu. Zamu kama wadanda suka aikata wannan aika-aika.

 

“Shugaban kasa ya damu matuka, kuma ya umarce mu da mu nemo wadanda suka aikata wannan aika-aika domin su fuskanci shari’a, muna aiki tare da gwamnatin jihar domin daukar tsarin da zai hana faruwar wannan mummunan lamari, lokaci ya yi da za a kawo karshen wannan hauka,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abubuwa 5 da ya kamata ku sani kan mutuwar Fafaroma Francis
  • Iyalen Surajo Malumfashi na Radio Nigeria Kaduna Yana Gayyatar Jama’a Zuwa Daurin Auren ‘Yar Sa
  • Iran Ba Ta Da Niyyar Tattaunawa Da Amurka A Fili Bainar Jama’a Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya?
  • Zaɓen 2027: An soma liƙa fastocin takarar shugaban ƙasa na Gwamnan Bauchi
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Gobara ta ƙone gidaje sama da 100 a sansanin ’yan gudun hijira a Borno 
  • Idan Shugaban Kasar Siriya Mai Ci Ya Taka Kasar Iraki Ana Iya Kama Shi
  • Amurka : Ana ci gaba da zanga-zangar kyamar tsare -tsare da manufofin gwamnatin Trump
  • Tawagar Gwamnati Ta Kai Ziyara Filato, Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Kashe-kashe A Jihar