Aminiya:
2025-03-04@03:14:54 GMT

APC ta kori tsohon Gwamnan Osun, Aregbesola daga jam’iyyar

Published: 1st, February 2025 GMT

Jam’iyyar APC a Jihar Osun, ta kori Tsohon Gwamnan Jihar kuma Tsohon Ministan Cikin Gida, Rauf Aregbesola, bisa zargin cin amanar jam’iyyar.

Wannan ya biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da shugabannin jam’iyyar na Ƙaramar Hukumar Ilesa ta Gabas suka gabatar.

Yadda Kano ta koma matattarar ’yan TikTok bayan Hisbah ta daina kamensu Muna da ƙarfin aljihun ɗaukar nauyin Taron Al-Ƙur’ani —Sheikh Bala lau

Sun nemi a ɗauki mataki a kan Aregbesola saboda zargin kafa ƙungiyoyin da ke raba kan jam’iyyar da yin haɗin gwiwa da jam’iyyun adawa don raunana APC a Osun.

A cikin wata wasiƙa da kwamitin zartarwa na APC na Osun ya aike wa shugaban jam’iyyar na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, sun bayyana cewa Aregbesola ya kafa wata ƙungiya mai suna “Omoluabi Caucus” ba tare da amincewar jam’iyyar ba.

Sannan ya yi furuci na ɓatanci ga shugabannin jam’iyyar, ciki har da Shugaba Bola Tinubu, tsohon gwamna Bisi Akande, da kuma tsohon gwamna Gboyega Oyetola.

Kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar ya rubuta wa Aregbesola wasiƙa, inda suka ba shi sa’o’i 48 ya mayar da martani kan zarge-zargen da ake masa.

Sai dai Aregbesola bai yi wani jawabi ba kan hakan ba, wanda ya sa jam’iyyar ta ɗauki matakin korarsa.

Wannan rikici ya ƙara nuna yadda rikicin cikin gida ke ƙara tsamari a jam’iyyar APC a Jihar Osun, musamman dangane da bambance-bambancen da ke tsakanin Aregbesola da wasu shugabannin jam’iyyar a matakin jiha da na ƙasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aregbesola Jihar Osun Kora Siyasa tsohon gwamna a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki domin tallafa wa mabuƙata a wannan wata mai albarka na Ramadana.

Mataimakin Gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ne ya ƙaddamar da rabon abincin a cibiyar Dandali da ke Ƙaramar Hukumar Fagge a jihar.

HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki

Bayanai sun ce gwamnatin jam’iyyar NNPP ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf da ta ƙaddamar da wannan shiri tana da burin raba abincin buɗa-baki ga mabuƙata masu azumtar watan Ramadana.

Gwamnatin ta ce an tanadi cibiyoyi 91 domin raba wa mabuƙata 91,000 abincin buɗa-baki duk rana nan da tsawon kwanaki 27 masu zuwa.

Domin tabbatar da samun nasara, gwamnatin ta ce ta ɗauki masu aikin girke-girke da za su riƙa dafawa sannan su raba wa mabuƙata abincin.

Mataimakin Gwamnan wanda shi ne ke jagorantar shirin raba abincin a bana, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka ƙaddamar da shirin, yana mai kiran waɗanda aka ɗora wa alhakin aikin su tabbatar da raba wa mabuƙata abincin a kan kari.

Aminiya ta ruwaito cewa, Mataimakin Gwamnan ya samu rakiyar wasu ƙusoshin Gwamnatin Kano wajen ƙaddamar da rabon abincin da suka haɗa da Kwamishinan Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya da Kwamishinan Harkokin Addini, Sheikh Tijjani Auwal da sauransu.

Gwamnatin Kano ta jaddada ƙudirinta na rage raɗaɗin al’umma musamman Musulmi a wannan wata mai falala.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Larabawa Sun Yi Tir Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji A Gaza
  • Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Shirin Ciyarwar Na Watan Ramadan
  • Yadda ’yan bindiga suka sace ɗalibai 4 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma
  • Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
  •  Hamas: Matakin Netenyahu Na Dakatar Da Shigar Kayan Agaji Cikin Gaza Keta Yarjejeniya Ne
  • Hamas Ta Yi Watsi Da Shawarar Isra’ila Na Tsawaita Matakin Farko Na Tsagaita Wuta A Gaza
  • Bayan Kwana 22, Tsohon Shugaban NYSC Tsiga Ya Kuɓuta A Hannun Ƴan Bindiga
  • Tsohon shugaban hukumar NYSC ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga
  • An Yi Musayar Yawu A Tsakanin Shugabannin Kasashen Amurka Da Ukiraniya A Fadar White House