Jami’in Kenya: Fasahar Sin Na Ingiza Samar Da Wutar Lantarkin Kenya
Published: 1st, February 2025 GMT
Kasar Kenya na amfani da damar ci gaban fasahar kasar Sin don kara dogaro da samar da wutar lantarki a kasar.
Darektan ma’aikatar kula da harkokin rarraba wutar lantarki ta kasar Joseph Siror ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, inda ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Nairobi, babban birnin kasar Kenya cewa, ababen more rayuwa a fannin samar da wutar lantakin kasar na kunshe da dimbin kayayyakin aiki daga kamfanonin kasar Sin irin su Huawei da rukunin Yocean.
“Sashen wutar lantarki na Kenya ya kuma ci moriyar musayar fasaha da kara sanin makamar aiki daga kamfanonin kasar Sin,” kamar yadda Siror ya bayyana a lokacin da kamfanin ya fitar da sakamakon rabin shekarar da ta gabata a ranar 31 ga Disamban 2024.
Siror ya kara cewa, masana’antun kasar Sin da dama sun yi nasara a takarar neman samar wa ma’aikatar wutar lantarki ta Kenya da na’urorin wutar lantarki saboda ci gaban fasaharsu da kuma karfi a bangaren hada-hadar kudi. Ya jaddada cewa, ta hanyar hadin gwiwa da kamfanonin kasar Sin, kasar Kenya ta samu damar samun hanyoyin samun kayayyakin wutar lantarki masu inganci kuma na zamani, da tsarin rarraba makamashi mai inganci, da na’urorin tantance yawan amfani da lantarki na zamani. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
কীওয়ার্ড: wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
An kori lakcara kan neman lalata da ɗaliba matar aure
Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) Bauchi ta sallami ɗaya daga cikin malamanta, Dokta Usman Mohammed Aliyu daga jami’ar bisa zargin neman yin lalata da wata ɗaliba matar aure da ke karatun digiri na biyu.
Idan dai ba a manta ba, Kamila Rufa’i Aliyu, ɗalibar Sashen koyon aikin injiniya ce, a shekarar bara ta roƙi mahukuntan Jami’ar ta hannun tsangayarsu da su binciki lamarin.
Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni An kama mata 2 na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka saceƊalibar ta kuma zargi Dakta Aliyu da yi mata barazanar rashin samun nasarar karatunta idan har ta ƙi amincewa da biyan buƙatarsa.
Malamin da ya samu labarin ƙarar da aka shigar da shi, an shigar da ƙarar a gaban kotu a kan zargin ɓata suna a kan wata ɗaliba, tsangayar da Jami’ar.
Amma Jami’ar a cikin Jaridarta (ATBU Herald) ta Afrilu 22, bugu na Vol. 39 lamba ta 5 ta bayyana cewa majalisar gudanarwa ta jami’ar ta kori Dakta Usman Mohammed Aliyu daga aiki a jami’ar.
Jaridar ta ce: “A zamanta na yau da kullun karo na 96 da aka gudanar a ranar Juma’a, 11 ga Afrilu, 2025, Majalisar ta amince da korar Dakta Aliyu bisa laifin neman yin lalata da ɗalibar.”
Rahoton ya ce korar ta biyo bayan wani rahoton da kwamitin ladabtarwa na manyan ma’aikatan ya yi wanda ya same shi da aikata laifin.
“Sanarwar ta ci gaba da cewa korar ta biyo bayan babi na 3, sashi na 1, (o) na sharuɗɗan manyan ma’aikatan jami’ar.