Leadership News Hausa:
2025-02-01@20:48:45 GMT

Jami’in Kenya: Fasahar Sin Na Ingiza Samar Da Wutar Lantarkin Kenya

Published: 1st, February 2025 GMT

Jami’in Kenya: Fasahar Sin Na Ingiza Samar Da Wutar Lantarkin Kenya

Kasar Kenya na amfani da damar ci gaban fasahar kasar Sin don kara dogaro da samar da wutar lantarki a kasar.

Darektan ma’aikatar kula da harkokin rarraba wutar lantarki ta kasar Joseph Siror ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, inda ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Nairobi, babban birnin kasar Kenya cewa, ababen more rayuwa a fannin samar da wutar lantakin kasar na kunshe da dimbin kayayyakin aiki daga kamfanonin kasar Sin irin su Huawei da rukunin Yocean.

An Kammala Aikin Tsugunar Da Mutane A Gundumar Tingri Ta Sin Bayan Bala’in Girgizar Kasa Ƴansanda Za Su Fara Tilasta Yin Insuran Motoci Daga 1 Ga Fabrairu

“Sashen wutar lantarki na Kenya ya kuma ci moriyar musayar fasaha da kara sanin makamar aiki daga kamfanonin kasar Sin,” kamar yadda Siror ya bayyana a lokacin da kamfanin ya fitar da sakamakon rabin shekarar da ta gabata a ranar 31 ga Disamban 2024.

Siror ya kara cewa, masana’antun kasar Sin da dama sun yi nasara a takarar neman samar wa ma’aikatar wutar lantarki ta Kenya da na’urorin wutar lantarki saboda ci gaban fasaharsu da kuma karfi a bangaren hada-hadar kudi. Ya jaddada cewa, ta hanyar hadin gwiwa da kamfanonin kasar Sin, kasar Kenya ta samu damar samun hanyoyin samun kayayyakin wutar lantarki masu inganci kuma na zamani, da tsarin rarraba makamashi mai inganci, da na’urorin tantance yawan amfani da lantarki na zamani. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Badala Ya Sa Jami’ar Oye Kafa Kwamitin Bincike

Kwamitin zai bincike kamar yadda aka bada sharuddan da za ta ayi amfani da su lokacin bincike, domin ta gano ta yaya lamarin maganganun da ake yadawa,da ake zargin abubuwan da suke da alaka da badana wanda mataimakin shugaban jami’ar ne aka ce akwai kokarin da ya yi domin ya sayi mukaman Bursar da rajistara, kana agano dalilin da yasa aka dauki maganar wadda yanzu ta zama abar maganar ta kafofin sadarwa na zamani.

Hakanan ma kwamitin an ba shi alhakin da ya yi bincike kan maganar da ake ta yadawa cewa shi Injiniya.Adebayo, musamman ma zargin da ake yi na shi mataimakin shugaban jami’ar a sake duba dukkan kokarin da aka yi da matakin da aka dauka wanda ‘yansanda, da shi kuma shugaban jami’ar na bya da sauran kan maganganun da Adebayo yay ikan mataimakin shugaban jami’ar.

Bugu da kari ta bada ayi bincike kan duk wani zargin da aka yi da duk abinda yake da alaka shi binciken.

“Hukumar jami’ar tana sa ran za ta yi amfani da rahoton binciken na kwamitin da ta kafa domin yin hakan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (5)
  • Zargin Badala Ya Sa Jami’ar Oye Kafa Kwamitin Bincike
  • Gwamna Radda Ya Samar Da Keke Napep Don Saukaka Zirga-zirga A Katsina
  • Dangantakar Cinikayya Da Sin Ta Budewa Afrika Kofar Samun Ci Gaba
  • NPA Da Kamfanin NLNG Za Su Kulla Hadakar Fitar Da Iskar Gas Ketare
  • Gwamnatin Katsina Ta Fitar Da Naira Miliyan Dubu 50 Domin Samar Da Ruwan Sha 
  • Tiktok Ya Yi Hadin Gwiwa A Kenya Don Bunkasa Tattalin Arziki Mai Nasaba Da Kirkire Kirkiren Jama’a
  • Wata uku uami’o’i ba su da wutar lantarki —SSANU
  • Rundunar Ƴansandan Kano Ta Kori Wani Jami’in Saboda Karɓar Na Goro