Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna ta biya fiye da Mahajjata dubu uku da suka kammala aikin Hajjin shekarar 2023 kudaden da Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON) ta mayar masu.

 

Mai Magana da Manema Labarai na hukumar, Yunusa Mohammed Abdullahi, shine ya bayyana hakan sannan ya kara da cewa an turawa kowane mahajjati ya karɓi sama da naira dubu sittin da ɗaya a asusunsa bakinsa.

 

Hukumar Alhazai ta Kasa NAHCON ta bayyana cewa an mayar da kudaden ne saboda katsewar wutar lantarki a lokacin da maniyyata ke Muna, wanda ya shafi tsarin sanyaya iska kuma hakan ya janyo musu matsala.

 

Hukumar Alhazai na Jihar Kaduna ta ta yaba da hakurin wadanda har yanzun basu same kudadensu ba, inda ya bayyana cewa jinkirin ya faru ne sakamakon wasu maniyyata ba su bayar da cikakken bayanan asusun ajiyarsu na banki ba.

 

Mallam Yunusa Abdullahi ya tabbatar da cewa an shirya sake fitar da wani zagaye na biyan kudaden a mako mai zuwa, kuma hukumar tana aiki tukuru don tabbatar da cewa dukkan alhazan 2023 da suka cancanta sun karɓi kuɗinsu.

 

Jami’in Hulɗa da Jama’a ya jaddada muhimmancin gabatar da bayanan asusun banki cikin lokaci, yana kira ga duk maniyyatan 2023 da har yanzu ba su karɓi kuɗinsu ba su tuntubi jami’in rijista na ofishin ƙaramar hukumarsu.

 

“Waɗannan bayanai suna da matuƙar muhimmanci don hanzarta mayar da kuɗi ga sauran Mahajjatan,” yana mai jaddada cewa KSPWA na da ƙudirin tabbatar da an biya dukkan kudaden Mahajjatan mudin sun banyarda bayanan asusun bankinsu akan lokaci.

 

Idan baza a manta ba, Shugaban Hukumar, Malam Salihu Abubakar, ya ce, “Mun fahimci muhimmancin mayarda waɗannan kudaden, kuma mun dukufa wajen tabbatar da cewa an kammala rabonsu cikin sauri da gaskiya.”

 

Sanarwar ta bayyana cewa, baya ga kammala biyan kudaden mayarwa na shekarar 2023, hukumar ta riga ta fara mai da hankali kan shirye-shiryen aikin Hajjin bana.

 

Rel/Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Biya Gwamnatin Jihar

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna

Gwamnan jihar Neja, Umaru Mohammed Bago, ya sanya dokar hana fita daga karfe 6 na yamma zuwa 6 na safe a Minna babban birnin jihar, sakamakon yawaitar hare-hare da kashe-kashen da ake yi a birnin. A cewar gwamnan, an takaita zirga-zirgar babura da masu tuka keke napep a tsakanin karfe shida na yamma zuwa karfe shida na safe. Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane 3, Ta Wanke Gonakin Shinkafa Sama Da Hekta 10,000 A Neja Sojoji Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Tare Da Kwato Makamai A Kano Bago ya bayyana hakan ne a yayin wani muhimmin taron tsaro da masu ruwa da tsaki suka yi da sarakunan gargajiya da shugabannin hukumomin tsaro a gidan gwamnati, ranar Talata. Ya ce, amma dokar ta kebe cibiyoyi da hukumomin kiwon lafiya. Ya bayyana cewa, sabon matakin na da nufin dakile matsalolin tsaro da ke kara tabarbarewa a babban birnin jihar. Gwamnan ya jaddada cewa, gwamnati ba za ta rungume hannu ba, yayin da masu aikata laifuka ke ci gaba da kai hare-hare da kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba. Ya kuma umurci gundumomi, ƙauye, da masu unguwanni da su sanya ido kan duk wadanda ke zaune a yankunan su. Ya kuma yi gargadin cewa, duk gidan da aka samu yana dauke da masu aikata laifuka ko masu safarar miyagun kwayoyi za a ruguza shi. A baya-bayan nan dai garin Minna ya sake samun koma-baya na ‘yan daba, da hare-hare, da kashe-kashe, lamarin da ke janyo firgici da damuwa a tsakanin mazauna garin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
  • 2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba
  • An Bayyana Filin Jirgin Sama Minna a Matsayin Mafita Ga Jiragen da ke sauka Abuja
  • Jirgin Farko Daga Minna Zuwa Abuja Ya Nuna Haɗin Gwiwar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi – Minista
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa
  • Motar hatsi ta kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Motar hatsi kashe masu bikin Ista 5 a Gombe