Aminiya:
2025-03-24@01:29:24 GMT

Abba ya karrama fitattun Kanawa 35

Published: 2nd, February 2025 GMT

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karrama wasu mutum 35 ’yan asalin Jihar Kano waɗanda suka yi fice a fannoni daban-daban na rayuwa.

Daga cikin waɗanda gwamnan ya karrama akwai janar-janar ɗin soji 19, Farfesoshi 6 da wasu fitattun Kanawa 10.

Asibitin Malam Aminu Kano ya hana motoci masu baƙin gilas shiga harabarsa Mahaifin ma’aikacin Aminiya ya rasu

Aminiya ta ruwaito cewa, an bayar da lambobin yabon ne ga fitattun mutanen maza da maza a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da ya gudana a Fadar Gwamnatin Kano ranar Asabar da daddare.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce waɗanda suka samu lambobin yabon sun yi fice a fannoni daban-daban na rayuwa kuma a dalilin haka an samu ci gaba musamman wajen inganta rayuwa da tattalin arzikin Jihar Kano da Nijeriya gaba ɗaya.

Abba ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa gwiwa da waɗannan zaƙaƙurai domin tabbatar da haɗin kai, zaman lafiya da kuma ci gaban Jihar Kano.

Gwamnan ya kuma hori matasa masu tasowa da su ɗauki waɗannan fitattun mutane a matsayin madubi wajen karkatar da alkalar rayuwarsu a fannonin ilimi daban-daban domin ɗaga martabar Kano a nan cikin gida da ƙetare.

Ya miƙa godiyarsa ga dukkan masu ruwa da tsaki da suka bayar da gudunmawa wajen ganin an samu nasarar gudanar da taron ciki har da Gwamnatin Tarayya ta ba da goyon baya.

Daga cikin waɗanda aka karrama akwai mace ta farko a Arewacin Nijeriya da ta zama Farfesa a fannin likitancin mata da ƙananan yara da mace ta farko a matsayin Kwamishinar ’Yan sanda da kuma Bakano kuma ɗan Nijeriya na farko da ke riƙe da muƙamin Shugaban Ƙungiyar Injiniyoyi ta Duniya.

A nasa jawabin, Shugaban Limaman Nijeriya, Sheikh Nasir Muhammad Adam, ya ƙalubalanci waɗanda aka karrama da su kasance alƙiblar da za ta zama haske ga matasa masu tasowa kafin cikar wa’adinsu a ban ƙasa.

Fitattun Kanawan da aka karrama sun haɗa da Air Marshal Hassan Bala Abubakar, Manjo-Janar M S Ahmed, Manjo-Janar IS Ali, Manjo-Janar A M Garba, Manjo-Janar Sani Sumaila Ibrahim, Manjo-Janar B U Yahya, Manjo-Janar S Y Bashir, Manjo-Janar U B Abubakar, Manjo-Janar Faruk Mijinyawa da Manjo-Janar Jamal Abdulsalam.

Sauran sun haɗa da Air Vice Marshal M Yusuf, Air Vice Marshal G A Bello, Air Vice Marshal B R Mamman, Air Vice Marshal SK Usman, Air Vice Marshal M S Ibrahim, Air Vice Marshal KM Umar, Rear Admiral Abdullahi Ahmad, Rear Admiral Aliyu Gaya da Rear Admiral Idi Abbas.

Ragowar waɗanda suka samu karrramawar sun haɗa da Farfesa Shehu Ahmad Said Galadanci, CON, Dokta Nasiru Sani Gwarzo, Yakubu Adamu Kofar Mata, DIG Dasuki Galadanchi, DDG DSS, Alhaji Ado Muazu, Farfesa Umma Abdullahi, Farfesa Hadiza Galadanci, Farfesa Nazifi Abdullahi Darma, Farfesa Hamisu Armayau Bichi, Farfesa Sagir Adamu Abass da Kwamishinar ’Yan sanda, CP Hajiya Hauwa Ibrahim.

Akwai kuma Rislanuddeen Muhammad, Injiniya Mustafa Balarabe Shehu, Arc. Hauwa Hassan Tudunwada, Ado kabiru Minjibir Mni da kuma Marwan Mustapha Adamu mni.

Bikin ya samu halarcin dattawa da kuma fasihai a fannonin rayuwa daban-daban daga garin na Kano.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Injiniya Mustafa Balarabe Shehu Jihar Kano kanawa Air Vice Marshal Manjo Janar

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adama

Jakadan dindindin na kasar Sin dake ofishin MDD a birnin Geneva da sauran hukumomin kasa da kasa a kasar Switzerland, Chen Xu, ya gabatar da jawabi a madadin kungiyar abokantaka ta inganta hakkin bil’adama, da tattaunawa da hadin gwiwa da sauransu, yayin taron MDD karo na 58 da ya gudana a jiya Alhamis. 

A cikin jawabinsa, jakada Chen ya bayyana damuwa game da mummunan tasirin da ra’ayin nuna bangaranci ya kawo, tare da tabbatar da bukatar aiwatar da ra’ayin cudanyar bangarori daban daban. Kazalika ya kamata a bi ka’idojin adalci, da gaskiya da kaucewa wariya a kwamitin kare hakkin bil’adama, ta yadda kare hakkin bil’adama zai gudana ta hanyar tsaro, da inganta hakkin bil’adama ta hanyar ci gaba, da kuma bunkasa hakkin bil’adama ta hanyar hadin gwiwa.

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun Kasar Sin Ta Bayar Da Rijiyoyin Burtsasai 66 Ga Al’ummomin Zimbabwe Dake Fama Da Karancin Ruwa

Jawabin nasa ya kunshi shawarwari guda uku na inganta ci gaban ayyukan kare hakkin bil’adama na duniya, inda da farko ya bukaci a tabbatar da gaskiya da adalci, sai na biyu dagewa wajen bude kofa, kana na uku shi ne tsayawa tsayin daka wajen samun nasara tare ta hadin gwiwa.

Bugu da kari, jawabin ya samu goyon bayan kasashe sama da 20, da suka hada da Rasha, da Cuba, da Eritrea da kuma Singapore, kuma kasashe masu tasowa sun yi tsokaci sosai a kan sa. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  • Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum
  • ’Yan daba sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna
  • Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adama
  • Gaggan Masu Garkuwa Da Mutane 10 Da Kayan Aikinsu Sun Shiga Hannu A Kano
  • Nasiru Ahali Shahararren masanin masana’antu a Kano ya rasu
  • Hajjin Bana: Maniyata 3, 155 Suka Yi Rijista a Kano
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • Gwamna Yusuf Ya Yi Sabbin Nade-Nade A Kano