Aminiya:
2025-04-14@18:29:17 GMT

Abba ya karrama fitattun Kanawa 35

Published: 2nd, February 2025 GMT

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karrama wasu mutum 35 ’yan asalin Jihar Kano waɗanda suka yi fice a fannoni daban-daban na rayuwa.

Daga cikin waɗanda gwamnan ya karrama akwai janar-janar ɗin soji 19, Farfesoshi 6 da wasu fitattun Kanawa 10.

Asibitin Malam Aminu Kano ya hana motoci masu baƙin gilas shiga harabarsa Mahaifin ma’aikacin Aminiya ya rasu

Aminiya ta ruwaito cewa, an bayar da lambobin yabon ne ga fitattun mutanen maza da maza a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da ya gudana a Fadar Gwamnatin Kano ranar Asabar da daddare.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce waɗanda suka samu lambobin yabon sun yi fice a fannoni daban-daban na rayuwa kuma a dalilin haka an samu ci gaba musamman wajen inganta rayuwa da tattalin arzikin Jihar Kano da Nijeriya gaba ɗaya.

Abba ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa gwiwa da waɗannan zaƙaƙurai domin tabbatar da haɗin kai, zaman lafiya da kuma ci gaban Jihar Kano.

Gwamnan ya kuma hori matasa masu tasowa da su ɗauki waɗannan fitattun mutane a matsayin madubi wajen karkatar da alkalar rayuwarsu a fannonin ilimi daban-daban domin ɗaga martabar Kano a nan cikin gida da ƙetare.

Ya miƙa godiyarsa ga dukkan masu ruwa da tsaki da suka bayar da gudunmawa wajen ganin an samu nasarar gudanar da taron ciki har da Gwamnatin Tarayya ta ba da goyon baya.

Daga cikin waɗanda aka karrama akwai mace ta farko a Arewacin Nijeriya da ta zama Farfesa a fannin likitancin mata da ƙananan yara da mace ta farko a matsayin Kwamishinar ’Yan sanda da kuma Bakano kuma ɗan Nijeriya na farko da ke riƙe da muƙamin Shugaban Ƙungiyar Injiniyoyi ta Duniya.

A nasa jawabin, Shugaban Limaman Nijeriya, Sheikh Nasir Muhammad Adam, ya ƙalubalanci waɗanda aka karrama da su kasance alƙiblar da za ta zama haske ga matasa masu tasowa kafin cikar wa’adinsu a ban ƙasa.

Fitattun Kanawan da aka karrama sun haɗa da Air Marshal Hassan Bala Abubakar, Manjo-Janar M S Ahmed, Manjo-Janar IS Ali, Manjo-Janar A M Garba, Manjo-Janar Sani Sumaila Ibrahim, Manjo-Janar B U Yahya, Manjo-Janar S Y Bashir, Manjo-Janar U B Abubakar, Manjo-Janar Faruk Mijinyawa da Manjo-Janar Jamal Abdulsalam.

Sauran sun haɗa da Air Vice Marshal M Yusuf, Air Vice Marshal G A Bello, Air Vice Marshal B R Mamman, Air Vice Marshal SK Usman, Air Vice Marshal M S Ibrahim, Air Vice Marshal KM Umar, Rear Admiral Abdullahi Ahmad, Rear Admiral Aliyu Gaya da Rear Admiral Idi Abbas.

Ragowar waɗanda suka samu karrramawar sun haɗa da Farfesa Shehu Ahmad Said Galadanci, CON, Dokta Nasiru Sani Gwarzo, Yakubu Adamu Kofar Mata, DIG Dasuki Galadanchi, DDG DSS, Alhaji Ado Muazu, Farfesa Umma Abdullahi, Farfesa Hadiza Galadanci, Farfesa Nazifi Abdullahi Darma, Farfesa Hamisu Armayau Bichi, Farfesa Sagir Adamu Abass da Kwamishinar ’Yan sanda, CP Hajiya Hauwa Ibrahim.

Akwai kuma Rislanuddeen Muhammad, Injiniya Mustafa Balarabe Shehu, Arc. Hauwa Hassan Tudunwada, Ado kabiru Minjibir Mni da kuma Marwan Mustapha Adamu mni.

Bikin ya samu halarcin dattawa da kuma fasihai a fannonin rayuwa daban-daban daga garin na Kano.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Injiniya Mustafa Balarabe Shehu Jihar Kano kanawa Air Vice Marshal Manjo Janar

এছাড়াও পড়ুন:

Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno

Ministan ya ce maganar da ya faɗa da farko wadda ba a ruwaito ta a daidai ba ita ce:

“E, lallai an samu cigaba a harkar tsaro a sassa daban-daban na ƙasar nan, ko da yake ba a kawar da duk wani aikin tashin hankali gaba ɗaya ba.

“Hukumomin tsaro suna aiki ba dare ba rana don tabbatar da cewa an shawo kan matsalolin da ake da su a wasu sassan Jihar Borno da wasu wurare.

“Haɗin gwiwar da muke gani tsakanin hukumomin tsaro, musamman a shekaru biyu da suka wuce, da kuma gagarumin zuba jari a kayan aiki da na’urorin zamani da ake yi, yana nuna yadda Gwamnatin Tarayya take ɗaukar batun tsaro da matuƙar muhimmanci.

“Gwamnatin Tinubu tana da ƙwarin gwiwar kawar da ayyukan ‘yan bindiga da ta’addanci a faɗin ƙasar.

“Nasarorin da hukumomin tsaro suka samu a cikin watanni 18 da suka wuce suna nuna cewa lallai Nijeriya tana komawa daidai a hankali a hankali.

“Gwamnati tana kira ga kowa da kowa, musamman gwamnatocin jihohi, da su haɗa hannu wajen kawar da ragowar ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka a duk inda suke.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • An Karrama Shugaban Qausain TV, Kanar Sani Bello Da Lambar Yabo
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  • Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina
  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Bam Ya Hallaka Mutane 8, Wasu da Dama Sun Jikkata A Borno
  • An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
  • An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi