Aminiya:
2025-04-14@20:51:47 GMT

Gwamnatin Najeriya za ta sake ƙara kuɗin lantarki

Published: 3rd, February 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta sanar das shirye-shiryenta na sake kara kudin wutar lantarki nan da watanni masu zuwa.

Ta bayyana cewa ana tsara karin ta yadda zai zo da tallafi ga masu karamin karfi cikin masu amfani da wutar.

Mashawarciyar Shugaban Kasa kan Makamashi, Olu Verheijen, ce ta sanar da hakan a Babban Taron Shugabannin Lantarki na Kasashen Afirka da ke gudana a Dar es Salaam, hedikwatar kasar Tanzania.

A yayin taron ta gabatar wa mahalarta da shirin na Najeriya na kashe Dala biliyan 32 domin inganta wutar lantarki zuwa shekarar 2030.

Batun karin na zuwa ne bayan a bara gwamnatin ta yi ninka kudin wuta sau uku ga kwastomomi da ke amfani da Band A.

A yanzu kuma kamfanonin rarraba wutar lantarki, wadanda basuka suka riga suka yi musu katutu, sun matsa wa gwamnatin lamba ta bari su kara kudi domin samar da wutar yadda za su share hawayen kwastomominsu.

A watan Afrilun 2024 Hukumar Wutar Lantarki ta Kasa (NERC) ta yi karin kudin wuta da kashi 300%, daga N68 zuwa N225 a kan kowane kilowat ga masu amfani da Band A.

Da yake sanar karin, Mataimakin Shugaban NERC, Musliu Oseni, ya ce kashi 15% na masu amfani da wutar ne ya shafa, kuma zai inganta samuwar wutar.

Hakazalika Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa idan aka ci gaba da biyan tallafi ga masu amfani da Band A, yawan kudin da gwamnati ke biya na tallafin a shekara zai karu zuwa Naira tiriliyan biyu.

Amma dai daga bisani an rage kudin zuaw N209.5.

Sabon kafin farashi

Game da sabon karin kudin, hadimar shugaban kasan ta bayyana cewa Najeriya na kokarin samar da tsarin samun wutar lantarki gwargwadon yadda aka biya kudin, domin jawo masu zuwa jari a bangaren.

Ta shaida wa taron cewa, “Daya daga cikin kalubalen da muke  kokari magancewa nan da ’yan watanni masu zuwa shi ne komawa tsarin shan wutar lantarki gwargwadon yadda aika biya.

“Da haka ne bangaren zai tara kudaden da ake bukata domin jawo ’yan kasuwa masu zuwa jari tare da kare talakawa da masu rauni daga cuta.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Karin kudin wuta Lantarki wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa

Tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ya shirya wani taron bikin cika shekaru 50 da kafuwa tare da gudanar da taron kasa karo na uku.

Taron wanda aka yi wa take da “Ilimi Mai Sauya Rayuwa Don Gaba: Fuskantar Sabbin Kalubale da Buɗe Damar Samun Ci gaba” ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki daga sashen ilimi.

Da take jawabi a wajen taron, Minista a ma’aikatar Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmed Sa’id ta bayyana cewa, a ƙoƙarin da gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ke yi na ƙarfafa tsarin ilimi, ya amince da kashe Naira biliyan 120 don bunƙasa shirin fasaha da koyon sana’o’i (TVET) a Najeriya.

Ministar ta kuma bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta amince da fitar da Naira biliyan 40 domin kammala aikin ɗakin karatu na ƙasa da aka yi watsi da shi, domin tallafawa bincike da cigaban karatu.

Farfesa Suwaiba ta ƙara da cewa, ma’aikatar ilimi ta tarayya ƙarƙashin jagorancin Minista Alausa ta ƙaddamar da Shirin Sabunta Hanyar Ilimi ta Najeriya (NESRI).

“Ina da burin mayar da Najeriya daga tattalin arzikin da ke dogara da albarkatu zuwa tattalin arzikin da ke dogara da ilimi, tare da rage yawan yara da ba sa zuwa makaranta, rage ƙarancin koyo, da samun  ƙara ƙwarewa.”

Yayin da yake buɗe taron, Shugaban Jami’ar Bayero Kano, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya bayyana nasarorin da sashen ya samu, inda ya ce ya samar da manyan mutane kamar ministocin ilimi biyu, shugabannin jami’o’i tara, da matan gwamnan jihar Kano guda uku, da sauran fitattun ’yan Najeriya da suka yi fice a fannoni daban-daban.

Yayin da yake yabawa taken taron da dacewarsa, Farfesa Sagir ya tabbatar da cewa jami’ar tana nan daram wajen tallafawa duk wani shiri da zai ɗaga matsayin ilimi zuwa na ƙasa da ƙasa.

A jawabinsa na maraba, Shugaban tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero Kano (BUK), Dakta Abubakar Ibrahim Hassan, ya jaddada yadda tsangayar ke  kokari wajen shirya harkokin ilimi da na kimiyya.

“Daga cikin nasarorin da Jami’ar BUK ta samu a kwanan nan akwai samun tallafin TETFUND guda biyu da kowanne ya haura naira biliyan 30, tare da lashe wani shirin koyar da harsuna biyu wanda Bankin Raya Musulunci da Hukumar Ilimin Firamare ta Kasa (UBEC) suka dauki nauyi.”

Taron ya yi armashi inda aka bayar da lambar yabo ga fitattun ‘yan Najeriya da suka hada da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da matarsa Farfesa Hafsat, da Minista a ma’aikatar Ilimi ta Jiha Farfesa Suwaiba, tsohuwar Ministar Ilimi Farfesa Rukayya, da Farfesa Isah Yahaya Bunkure da wasu da dama.

Daga Khadija Aliyu 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Guguwar Kudin Fito Na Gwamnatin Trump: Dabara Ko Hauka?
  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • Dalilai 12 Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmanci Ga Al’umma (1)