Aminiya:
2025-02-22@06:23:48 GMT

Sarkin Jiwa a Abuja ya yi rashin mahaifiya 

Published: 5th, February 2025 GMT

Mai martaba sarkin Jiwa a yankin birnin tarayya Abuja, Alhaji Idris Musa ya yi rashin mahaifiyarsa mai suna Hajiya Ramatu Ibrahim.

Ta rasu ne a safiyar Lahadi kamar yadda sarkin malamai na masarautar malam Jibrin Yakubu Adam ya tabbatarwa Aminiya.

Hajiya Mai Babbar Ɗaki, kamar yadda ake yi mata laƙabi, ta rasu ta bar ‘ya’ya huɗu da kuma jikoko sama da 30.

Ya ce, an gudanar da janaiza tare da binneta a Babbar maƙabartar Garin Jiwa a ranar ta Lahadin.

Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba

Cikin waɗanda suka halarci jana’izar akwai Sarkin Bwari Alhaji Muhammad Auwal Ijakoro, da Gomo na Kuje Alhaji Haruna Tanko Ibrahim, da Sarkin Pai Alhaji Abubakar Sani Pai, sai kuma shugabannin ƙananan hukumomin Birnin Abuja da kewaye (AMAC) da kuma takwaransa na Abaji, wato Mista Christopher Zakka Mai Kalangu da malam Abubakar Umar Abdullahi.

A yayin ziyarar ta’aziyya da ya kai ga sarkin Jiwa a ranar Litinin, Sarkin Rubochi da ke yankin Kuje a Abuja, Alhaji Muhammad Ibrahim Pada, ya bayyana marigayiyar a matsayin uwa ta gari da ta samar da kyawawan tarbiyya abin koyi ga ‘ya’yanta, inda ya yi addu’ar Allah Ya gafarta mata da kuma yi mata rahama da Aljannah.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bwari Jiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar

Shugaban kungiyar Hamas Khalilul-Hayyah, ya fadi cewa; A ranakun Alhamis da Asabar masu zuwa ne za a mikawa ‘yan mamaya fursunoni rayayyu da kuma wasu gawawwaki a cikin bude wani shafin na musaya.

 A jiya Talata ne dai Khalilul-Hayyah ya sanar da cewa, a bisa yadda aka cimma matsaya a musayar farko da aka yi, a cikin mako na shida daga kulla yarjejeniya, za a shiga wani sabon shafin na  gaba na musayar fursunoni.

 Khalil Hayya ya kuma ce a ranar Asabar din mai zuwa ne za a mika sauran fursunoni rayayyu da su ka saura, kamar yadda aka cimma matsaya da adadinsu shi ne 6, biyu daga cikinsu ana rike da su ne tun 2014, yayin da ‘yan mamaya za su saki sauran fursunonin da suke rike da su.

Shugaban na kungiyar Hamas ya bayyana hakan da cewa, yana nuni da yadda kungiyar take aiki da yarjejeniya, tare da yin kira da a tilasta HKI ta yi aiki da sharuddan yarjejeniyar ba tare da jan kafa ba. Haka nan kuma ya bayyana cewa kungiyar ta Hamas tana cikin shirin ko-ta –kwana na shiga shafi na gaba wanda shi ne dakatar da yaki da kuma janyewar sojojin mamayar daga Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu sassan Abuja za su kasance cikin duhu a ƙarshen mako – TCN
  • Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa
  •  Jagora: Siyasar Kasar  Iran  Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta
  • Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu
  • Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan Tsaro
  • Sarkin Qatar Ya Iso Tehran A Yau Laraba
  • Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar