HausaTv:
2025-04-25@11:36:33 GMT

Duniya Na Ci Gaba Da Mayar Wa  Da Donald Trump Martani Akan Gaza

Published: 6th, February 2025 GMT

Kasashen larabawa masu kawance da Amurka sun kasance a sahun gaba wajen mayarwa da shugaban kasar Amurkan martani, bayan da ya bayyana cewa kasarsa za ta shimfida ikonta a Gaza, bayan fitar da Falasdinawa da Gaza.

Gabanin wannan sanarwar ta  Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa ya tuntubi kasashen Jordan da Masar masu makwabtaka da Falasdinu da su karbi bakuncin mutanen Gaza na wani lokaci har zuwa sa’adda za a gyara wajen.

Masar da Jordan sun yi watsi da wannan shirin da suke dauka a matsayin wata dabara ce ta fitar da Falasdinawa daga cikin kasarsu, da maye gurbinsu da yahudawa ‘yan share wuri zauna.

A wani bayani da kungiyar hadin kan Larabawa ta fitar ta bayyana cewa; Abinda  Trump din ya fada yana da tayar da hankali, kuma yin kira ne ga hargitsa yankin.

Kungiyar mai kasashe mambobi 22 ta kuma kara da cewa, wannan shawara da Trump ya fito da ita, tana cin karo da dokokin kasa da kasa.

Ita ma kungiyar kasashen musulmi ta ( OIC) da take wakiltar musulmin duniya miliyan 1.5, ta ce za ta ki amincewa da wannan shawarar wacce take son sauya tsarin zamantakewa na wannan yankin.

Wasu daga cikin kasashen wannan yankin abokan Amurka da su ka yi watsi da shirin na Trump na  korar Falasdinawa daga Gaza    sun hada Saudiyya, Jordan, Masar, Katar da Hadaddiyar Daular Larabawa, sai kuma Turkiya.

Ita ma MDD ta bayyana cewa hanyar kawo karshen batun Falasdinu shi ne abinda ta kira; Kafa kasashe biyu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya

A ranar 17 ga watan Afrilun da muke ciki ne wakilai ko ministocin noma na kasashen kungiyar BRICS suka taro a Brazilian a kasar Brazil inda suka rantaba hannu kan shelanta shirin namusamman na bunkasa ayukan noma da kuma harkokin samar da abinci da kuma wadatar da shi ga kasashen duniya farko ga kasashen kungiyar.

Shirin dai ya hada da na shekara ta 2021-2024 da kuma na 2025-2028, wadanda kungiyar zata aiwatar da su tare.

Shirin ya hada da bunkasa ayyukan noma da samar da wuraren ajiye kayakin noma da kuma taimakawa kananan ayyukan noma a kasashen kungiyar saboda smaar da manoma wadanda zasu yi noma mai yawa nan gaba. Sannan rage abubuwan da ke hana ayyukan noma ci gaba a cikin kasashen kungiyar .

Kasashen kungiyar BRICS dai suna da kasha 54.5 % na yawan mutane a duniya, sannan suna noman 1/3 na filayen noma a duniya, wanda zai bada damar aiwatar da dukkan wadannan ayyuka da sauki da kuma sauri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • Faransa ta jaddada aniyarta na ci gaba da tattaunawar nukiliyar iran
  • Sojan HKI Ya Halaka A Gaza
  • Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • Al’ummar Gaza Suna Tsananin bukatar Agaji Da Kiran A Tilastawa Gwamnatin Mamayar Isra’ila Bude Mashigar Yankin
  • Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya
  • ECOWAS Zata YI Taro A Ghana Don Tattauna Batun Niger, Mali Da Burkina Faso
  • Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa