Hujjar mu a nan ita ce, kundin tsarin mulkin Nijeriya, sama yake da kowanne dan kasar da kuma sauran dokokin kasar, duba da cewa, kundin ya bayar da damar a yi Shari’ar a bisa adalci kuma a bayyane, ga wadanda ake tuhumar da aikata laifi.

Bugu da kari, dole ne mu tuhumi matakan da mahukuntan kasar suka dauka na yiwa wadanda ake tuhumar Shari’ar a, asirce.

Akwai dimbin tambayoyi a zukatan ‘yan Nijeriya wanda kuma suke bukatar amsa, misali, a ina ne aka cafke su? ta yaya ne, aka kama su? yaushe ne, aka gurfanar da su, a gaban Kotu? Shin an barsu sun dauki Lauyoyin da za su tsaya masu gaban Kotu? har tsawon wanne lokaci ne, suke ci gaba da fuskantar Shari’a kuma kan wanne laifi ne, Kotu ke tuhumarsu?, me ya sanya ake yi masu Sharia’a a, asirce?

Tabbas, ‘yan Nijeriya na bukatar amsar wadannan tambayoyin, duba da cewa, kamata ya yi, a ce, ana yin masu Shari’ar bisa bin ka’ida, ko dai mutum dan kasa ne ko kuma bakin haure ne, ya kamata a ce, ana yi masu Shari’ar a bayya ne.

Yi wa mutanen, Shari’ar a, asirce ya savawa ka’ida duba da cewa, kundin tsarin mulkin Nijeriya, ya tanadi a bai wa, duk wanda ake zargi, ‘yancin da yi masa adalaci, kan tuhumar da ake yi masa.

Wannan Shari’ar da ake yiwa mutanen a asirce, hakan ya jefa ‘yan Nijeriya a cikin  bakin duhun, sanin  hakikanin yadda Shari’ar ke tafiya, hujojin da aka gabatar a kansu a gaban Kotu tare da kuma cewar, wadanda Kotun ke tuhuma, a kan wanne takamaiman laifi ne, aka gurnar da su kuma wanne irin hukuncin da aka yanke masu.

Hakan ya nuna cewa, rashin bin ka’ida a yi masu Shari’ar, tare da taka dokar kasa da kuma take ‘yancin ‘yan Adam.

Kazalika, hakan ya sanya nuna rashin aminta da Gwamnatin Tarayya, na cewa, ko za yi hukuncin bisa gaskiya.

Abin tambaya a nan shi ne, ta yaya irin wadannan gungun tantiran ‘yan ta’addar, musamman ‘yan ta’addar Boko Haram da suka fara aikita ta’addancin su tun a 2009, a kuma ce wai za yi masu Shari’a asirce?

‘Yan Nijeriya na bukatar sanin shi wadanne mutane ne, ke taimakawa ‘yan ta’addar wajen aikata ta’asarsu.

A gafe daya kuma, ‘yan ta’addar na ci gaba da kai farmaki ga sansanonin dakarun soji tare da kuma hallaka su da kuma kashe sauran fararne Hula, ciki har da dattijai, mata da kuma yara, inda ta’asar ta su, ta mayar da yaran marayu, matan kuma suka zama zawarawa ba tare da sun aikatawa ‘yan ta’addar wani laifi ba.

‘Yan ta’addar, sun zama tamkar, wasu mala’ikun mutuwa sanadiyyar kisan da suke yi, hakan ya janyo tarwatsa mafarkin wadanda lamarin ya rutsa da su da kuma tarwatsa su, daga matsugunan su, da suka gada tun daga kaka da kakanni.

Har zuwa yau, ‘yan makarantar Boko, musamman ‘ya’ya mata ana ci gaba da yin garkuwa da su, a wasu sassan kasar nan, tare da kuma yadda ‘yan ta’addar ke tilasta su, su aure su da kuma sanya su a aikin bauta.

‘Yan Nijeriya na ci gaba da hadiye fishinsu duba da cewa, wadanda suka dauki nau’yin ‘yan ta’addar da suka aikata masu ta’asar, amma Gwamnatin Tarayya ta yi uwa ta kuma yi makarviya, wajen kin yiwa ‘yan ta’addar da masu daukar nauyinsu Shari’a a asirce.

A namu ra’ayin domin ‘yan Nijeriya su yi ammana da Shari’ar da ake yiwa wadnda ake tuhumar a, asirce, ya zama wajbi Gwamnatin Tarayaya ta bayyana su, ta hanyar wallafa sunayensu, hotunansu, kanannan hukumomin da suka fito da kuma jihohin su na haihuwa, irin laifin da suka aikata aka kaisu gidan kaso da kuma irin hukuncin da aka yanke masu, a cikin a Jaridun kasar.

Yin hakan zai bai wa kamfanoni masu zaman kansu yanke duk  wata nau’in hada-hadar kasuwanci da su da kuma hana hukumomin gwamnati daukar su, aiki.

Muna shawartar Gwamnatin Tarayya cewa, da ta sake yin tunani, kan dabarun da ta dauka, na yiwa wadnada ake tuhumar, Shari’ar asirce.

Daukar wannan shawarar na da matukar mahimmanci, musamman domin a tabbatar da yin gaskiya da adalci tare da kuma kare kimar ‘yancin Adam da kuma girmama  dokar kasa.

Hakazalika, Gwamnatin Tarayya, ta tabbatar da yi masu Sharia’r bisa gaskiya, a bar su, su dauki Lauyoyi da za su tsaya masu, kuma hujjojin da aka gabatar kan zarginsu, su kasance na gaskiya ne, wadanda kuma za a iya gabatarwa, a gaban Kotu.

Abu ne, mai kyau a yaki da ta’addanci, amma ya kamata a yi hakan, ta hanyar mutunta ‘yancin daidaikun mutane, tabbatar da yin gaskiya da adalci da kuma mutunta, ‘yancin ‘yan Adam.

Batun yi wa masu aikata ta’addanci Shari’a ko kuma masu daukar nauyin aikata ta’addanci a kasar nan a, asirce, abu ne da ya savawa turbar mulkin Dimokiradayyar Nijeriya.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Shari a Gwamnatin Tarayya a yi masu Shari yan Nijeriya yan ta addar masu Shari a tare da kuma duba da cewa ake tuhumar

এছাড়াও পড়ুন:

Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya

Wasu manyan ’yan Nijeriya da suka tafi Umarah sun yi wa Gwamnan Katsina Dikko Umar Radda ta’aziyya a Saudiyya.

A safiyar Lahadi ce dai Allah Ya karɓi rayuwar mahaifiyar Gwamnan, Hajiya Safara’u Umaru Baribari bayan shafe tsawon lokaci tana jinya a Jihar Katsina.

Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci

Bayan rasuwar ce gwamnoni da wasu fitattun ’yan siyasa da a halin yanzu suna ƙasa mai tsarki suka kai wa Gwamna Radda ziyara domin jajanta masa dangane da wannan babban rashi.

Daga cikin gwamnonin akwai Mohammed Umar Bago na Jihar Neja, da Farfesa Babagana Zulum na Jihar Borno da Gwamna Uba Sani na Kaduna, da Dauda Lawal Dare na Zamfara da kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe

Sauran fitattun ’yan siyasar da suka ziyarci Gwamna Radda sun haɗa da Shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, da tsohon Gwamnan Bauchi, Ahmed Mu’azu.

Akwai kuma fitaccen attajirin nan kuma ɗan kasuwa, Alhaji Dahiru Mangal da kuma tauraron tawagar ƙwallon ƙafar Nijeriya ta Super Eagles, Ahmed Musa da su ma suka jajanta wa gwamnan a kan rashin.

Dukkansu sun bayyana alhini tare da roƙon Allah Ya jiƙan Hajiya Safara’u Ya sa ta huta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe
  • Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul
  • SDP: Ba Mu Yi Wa Kowa Alƙawarin Takarar Shugaban Ƙasa Ba
  • Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD
  • UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • Dole Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Ta Daina Barazana Ga Masu Sukar Ta – Amnesty
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar