Aminiya:
2025-02-22@06:21:40 GMT

Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki a Katsina

Published: 7th, February 2025 GMT

Majalisar Karamar Hukumar Jibiya a Jihar Kastina ta biya wa al’ummarta kudin wutar lantarki a kowane wata.

Shugaban Hukumar, Alhaji Bishir Sabi’u na cewa nan gaba za a kammala aikin layin da aka ware musu na musamman na Kamfanin Wutar Lantarki ta Kasa (TCN).

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito shi yana cewa karamar hukumar ta riga ta hada garin Jibia da layi na musamman na TCN domin garin ya rika samun wutar yadda ya kamata.

Ya ce, “duk da cewa an yi gwajin wutar, amma ba a riga an kammala aikin layin na TCN ba, kuma da ya fara aiki, al’ummar garin za su fara samun wutar lantarki tsawon awa 24.”

’Yan sanda sun sa dokar hana yawon dare a Gombe NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai

Honorabul Sabi’u wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Alhaji Mohammed Lawal-Jibia, ya ce karamar hukumar ta kulla yarjejeniyar da Kamfanin Wutar Lantarki na Kano (KEDCO), domin biyan kudin wutar lantarki Naira miliyan biyu ga al’umma a duk wata.

Ya ce sun dauki matakin ne domin rage wa jama’a wahalar da suke fama da ita ta tsadar rayuwa, musamman lura da yadda matsalar tsaro ta addabi yankin.

Ya bayyana cewa mma duk da haka, masu sana’o’in da ke jan wutar lantarki sosai ba sa cikin masu cin gajiyar tagomashin.

Alhaji Mohammed Lawal-Jibia ya sanar da hakan ranar Alhamis a yayin karbar bakuncin shugabannin Kungiyar ’Yan Jarida ta Kasa (NUJ) a kai kai masa ziyarar aiki.

Shugaban Karamar Hukumar ya bayyana cewa an samu wannan nasara da makamancin sa aka samu a bangaren noma da ilimi da sauransu ne da sahalewar Gwamna Dikko Radda.

A cewarsa, matsalar tsaro a karamar hukumar ta ragu sosai, yana ai cewa gwamnan bai taba yin watsi da bukatar al’ummar Jibia kan sha’anin tsaro ba.

Hasalima, gwamnan ya ba da fili da za a gina gidaje 152 domin sake tsugunar da ’yan gudun hijira a karamar hukumar.

Jibia na daga cikin kananan hukumomin Jihar Katsina mafiya fama da hare-haren ’yan ta’adda, inda da wuya a yini ba tare da hari ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lantarki karamar hukumar wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Legas ta bayar da umarnin a ƙwace Dala miliyan 4.7 da Naira miliyan 830 da wasu kadarori da dama da ke da alaƙa da tsohon Gwamnan babban bankin Najeriya (CBN) Godwin Emefiele.

Da yake yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai shari’a Yellim Bogoro, wanda a baya ya yi watsi da buƙatar kama Emefiele, ya amince da buƙatar hukumar yaƙi da yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta EFCC, wadda lauya Bilkisu Buhari-Bala ta wakilta.

’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida

Kuɗaɗen da a halin yanzu gwamnatin tarayya ta ƙwace, sun kasance a cikin asusun bankunan: First Bank, Titan Bank da Zenith Bank da wasu mutane da hukumomi suke kula da su da suka haɗa da: Omoile Anita Joy, kamfanin Deep Blue Energy Serɓice Limited, kamfanin Exactquote Bureau De Change Ltd, Kamfanin Lipam Investment Services Limited, kamfanin Tatler Services Limited, kamfanin Rosajul Global Resources Ltd, da kamfanin TIL Communication Nigeria Ltd.

Kaddarorin da aka ƙwace na wucin gadi sun haɗa da:  Ɗakuna 94 na wani bene mai hawa 11 da ake ginawa a 2 Otunba Elegushi 2nd Aɓenue, Ikoyi, Legas; da AM Plaza, ofisoshi mai hawa 11 a ginin Otunba Adedoyin Crescent, Lekki Peninsula Scheme 1, a Legas; da Imore Industrial Park 1 a Esa Street, Imoore Land, a Ƙaramar Hukumar Amuwo Odofin a Legas; Mitrewood and Tatler Warehouse kusa da Elemoro, Village Owolomi, Ibeju-Lekki LGA, Lagos; da kadarori biyu da aka saya daga kamfanin Chevron Nigeria, da ke cikin rukunin gidaje na Estate Lakes a Lekki da ke Legas.

Mai shari’a Bogoro ya bayyana cewa, duk waɗannan kadarori da kuɗaɗe ne na wasu ayyuka da suka saɓawa ƙa’ida, waɗanda gwamnatin tarayyar Najeriya za ta iya kwace  su.

Alƙalin ya ce: “Na ga cewa ayyukan waɗanda ake ƙara a nan ba halastattu be ne. Me zai sa su samu matsalar dala nan take, Godwin Emefiele ya bar CBN a matsayin gwamnan Banki kuma an kasa biyan albashi?

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ke ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
  • Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Dauki Nauyin Dalibai 80 Da Ke Manyan Makarantu
  • Wasu sassan Abuja za su kasance cikin duhu a ƙarshen mako – TCN
  •  Malaysia: An Bude Kiran Yanke Sayen Kere-kere Kamfanin “Tesla” Na Elon Musk
  • An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • Iran Ta Yi Tir Da Shugaban Hukumar IAEA Saboda Sanya Siyasa Da Daukan Bangare A Jawansa Na Baya Bayan Nan
  • Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba