Kasar Saudiyya ta jaddada matsayinta na kin amincewa da kalaman Netanyahu dangane da korar Falasdinawa daga Zirin Gaza

Kasar Saudiyya ta jaddada yin tofin Allah tsine, da kuma karfafa kin amincewa da kasashen Larabawa suka yi dangane da furucin Benjamin Netanyahu kan neman korar al’ummar Falastinu daga kasarsu ta gado.

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Saudiyya ta fitar a yau Lahadi, ta jaddada cewa: Saudiyya ta tabbatar da yin watsi da irin wadannan kalamai da ke da nufin karkatar da hankali daga jerin laifukan da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da yi kan Falasdinawa a Gaza, ciki har da kisan kare dangi da ake yi musu.

Sanarwar ta kara da cewa: Wannan tunani na tsattsauran ra’ayi na ‘yan mamaya baya daukan Falasdinu a matsayin kasar Falastinu wacce take matsayar kasar gado da tarihi da shari’a suka tabbatar da hakan, kuma ‘yan mamaya ba su la’akari da cewa tun farko al’ummar Falastinu sun cancanci rayuwa; Don haka suka rusa yankin Zirin Gaza gaba daya, tare da kashe mutane fiye da dubu 160, wadanda akasarinsu yara da mata ne, ba tare da kiyaye dokokin kasa da kasa da na hakkin dan Adam ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Saudiyya ta

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen

Jiragen yakin Amurka sun kai sabbin hare-hare kan wasu yankunan a kasar Yemen a safiyar a jiya Asabar, wadanda suka Baida Sa’ada da kuma Hudaidah wadanda sune sake zafafa yaki a ciki kasar na baya-bayan nan.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kafafen yada labarai na kasar ta Yemen na fadar cewa jiragen yakin kasar ta Amurka sun kai  hare-hare har 5 a kan makarantar koyon sana’o’ii na Al-sawma  da ke lardin  Al-Bayda a jiya Asabar .

Labarin ya kara da cewa makarantar ita ce babbar makaranta a yankin, kuma cibiyar ilmi mafi girma. Har’ila yau labarin ya bayyana cewa jiragen yakin kasar ta Am,urka sun kai hare-hare har guda 3 a kan garin Al-Sahleen daga cikin yankunan Kitif da kuma Al-Bogee daga cikin lardin Sa’ada.

Labarin ya kara da cewa wannan yankin yana daga cikin yankunan da ake fafatawa da sojojin  Amurka, kuma suna yawaita kan hare-hare a cikinsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • Shugaban Burkina Faso Ya Yi Fatali Da Tayin Saudiyya Na Gina Masallatai 200 A Kasarsa
  • Sin Ta Yi Allah-wadai Da Karin Harajin Amurka Ta Kuma Jaddada Goyon Bayanta Ga Ka’idojin WTO 
  • Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • MDD Ta Bukaci Taimako Dangane Rikicin Sudan Wanda Ya Isa Kasar Chadi
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing