Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-02-21@14:55:52 GMT

Jihar Bauchi Zata Tarbi Taron Karrama Sir Ahmadu Bello Karo Na 11

Published: 11th, February 2025 GMT

Jihar Bauchi Zata Tarbi Taron Karrama Sir Ahmadu Bello Karo Na 11

 

Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello ta sanar da cewa za a gudanar da taron Karrama Sir Ahmadu Bello karo na 11 a ranar Asabar, 22 ga Fabrairun 2025, a Bauchi.

 

 

Wannan taron, wanda ke tunawa da rayuwa da gado na Sir Ahmadu Bello KBE, Sardaunan Sokoto da Firaministan tsohuwar Yankin Arewa, zai hada da jerin tattaunawa da ayyukan da zasu mayar da hankali wajen magance kalubalen tattalin arzikin yankin.

 

 

Taken taron na bana, “Alherin Duniya: Sauyw Albarkatun Halitta na Arewa zuwa Cigaba Mai Dorewa”, na zuwa ne a lokacin da ake fuskantar karin damuwa kan talauci da rashin aikin yi da rashin ci gaba duk da kasancewar Arewa na da yalwar albarkatun halitta.

 

 

Za a tattauna yadda yankin zai iya amfani da gonakin noma da ma’adinai da albarkatun ruwa wajen samun ci gaban tattalin arzikin da zai dore.

 

 

Wannan taron na tsawon mako guda zai hada da horo na kwarewar zamantakewa ga matasa a Jihar Bauchi da gabatar da tallafin karatu ga dalibai ‘yan asalin jihohin Arewa a makarantu na gaba da sakandire da kuma ba da kyaututtuka ga mutanen da suka cancanta a fannonin al’umma.

 

 

Tsohon Daraktan Gudanarwa na Bankin Duniya, Dr. Mansur Mukhtar OFR, zai gabatar da jawabi, yayin da His Excellency Senator George Akume, Sakataren Gwamnatin Tarayya, zai kasance matsayin baƙo na musamman.

 

His Excellency Alh. Muhammadu Inuwa Yahaya CON, Gwamnan Jihar Gombe ne wanda zai jagoranci taron, tare da Gwamnan Jihar Bauchi, His Excellency Sen. Bala Mohammed CON, a matsayin babban mai masaukin baki.

 

 

Ana sa ran manyan baki a wurin taron su hada da gwamnonin jihohi da ‘yan majalisar dokoki da ministoci da sauran manyan masu ruwa da tsaki, wanda ke nufin haɓaka tattaunawa mai ma’ana da dabaru masu amfani domin bude damar ci gaban tattalin arzikin Arewa.

 

Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello tana ci gaba da aikinta na inganta ilimi da cigaban ɗan adam, da cigaban tattalin arziki a Arewa, a cikin girmamawa da gado na marigayi Sardauna.

 

Daraktan gidauniyar, Engr. Dr. Abubakar Gambo Umar, ya bayyana farin cikinsa dangane da wannan taron, yana mai jaddada muhimmancin albarkatun halitta na Arewa wajen tsara makomar yankin.

 

“Yankin Arewa na da yalwar albarkatun halitta da noma da ma’adinai da ruwa wanda zai iya zama babban dama don haɓaka ci gaban dake dorewa,” in ji shi.

 

“Amma wannan damar za a iya cimma ta ne kawai idan muka ɗauki hanyar gudanarwa ta haɗin gwiwa da cikakken tsarin kula da albarkatu, domin tabbatar da cewa ci gaban yana faɗaɗa ga dukkanin masu ruwa da tsaki,” ya ƙara da cewa.

 

Dr. Umar ya kuma bayyana muhimmancin taron Karrama Sir Ahmadu Bello a matsayin dandalin tattaunawa a kan waɗannan kalubale.

 

Ya kara da cewa, “Wannan jerin taron yana cikin muhimmancin gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello na ƙarfafa tattaunawa mai ma’ana a kan shugabanci da cigaba mai dorewa da haɓaka tattalin arziki.

 

 

Ya ce, “yana da muhimmanci mu haɗa muryoyi daban-daban daga gwamnati da ɓangarori masu zaman kansu, da ƙungiyoyin farar hula don ƙirƙirar dabaru masu amfani wajen ci gaban yankin.”

 

 

Khadija Kubau

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi Zata Tarbi Taron Karo Karrama

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya kaddamar da shirin Da’awah na mata a hukumance, domin karfafawa mata ilimin addinin musulunci, da karfafa alakar iyali, da kyautata rayuwa a tsakanin.

Da yake jawabi a wajen bikin a Dutse, Gwamna Namadi ya jaddada muhimmiyar rawar da mata ke takawa wajen tsara tarbiyar al’umma da kyawawan dabi’u.

“Kamar yadda aka sani, kusan rabin al’ummar jihar Jigawa mata ne, wadanda suka hada da iyayenmu, da ‘ya’yanmu, wanda hakan ya sa ya zama wajibi a kara zage dantse domin kula da addini da kuma tarbiyyarsu”.

Malam Umar Namadi ya jaddada wajibcin addini da ya rataya a wuyan maza na tallafa wa mata da bi da su hanyar shiriya, inda ya bukaci maza da su kyautata mata kamar yadda addini ya tanadar.

Ya kuma yabawa ma’aikatar harkokin mata da ci gaban al’umma ta jiha bisa jajircewarta wajen samun nasarar shirin, tare da yabawa babbar rawar da uwargidansa Hajiya Hadiza Umar Namadi ta taka wajen daukar nauyin shirin.

Namadi ya kuma yabawa Majalisar Malamai ta Jiha da dukkan masu ruwa da tsaki, bisa kokarin da suka yi wajen bunkasa tsarin da samar kayan aikin.

“Na yaba da kokari da sadaukarwar da kuka nuna wajen tabbatar da samun nasarar wannan shiri, Allah ya karbi dukkan gudunmawar da kuka bayar a matsayin Sadaqatul Jariyya.”

Ya kuma bukaci dukkan mahalarta taron da su rungumi shirin da zuciya daya, tare da jaddada muhimmancin ikhlasi, da kyawawan halaye, da hakuri da ayyukan Da’awah, tare da karfafa musu gwiwa da su rungumi koyarwar Alkur’ani mai girma.

Gwamnan ya kuma jaddada kudirin gwamnatinsa na tallafawa ci gaban mata, tare da yin kira ga shugabannin addini da na al’umma da su ci gaba da gudanar da shirin a dukkan kananan hukumomin jihar.

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, shirin wanda hadin gwiwa ne tsakanin Gwamnatin Jihar Jigawa, Majalisar Malamai ta Jiha, da sauran shugabannin addini da na al’umma, na neman ilmantar da mata kan koyarwar addinin Musulunci, da inganta rawar da suke takawa wajen ci gaban iyali da ci gaban al’umma tare da samar da zaman lafiya, da kyautatawa da mutunta juna.

A karkashin shirin an zabo mata 574 daga sassa daban-daban na jihar.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tara Naira 16 a taron ƙaddamar da littafin IBB
  • Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu
  • Ministoci Za Su Fara Gabatar Da Rahoton Ayyuka A Taron Manema Labarai  
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa
  • Nijar: Taron Kasa Ya Bukaci Sojoji Su Yi Mulkin Rikon Kwarya na Shekara 5
  • Saudiyya ta Gayyaci Kasashen Larabawa Kan Batun Kan Batun Gaza
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
  • Kamfanonin Sin Masu Zaman Kansu Na Taka Rawar Gani Ga Bunkasuwar Tattalin Arzikin Duniya
  • Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.