Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya
Published: 12th, February 2025 GMT
An cafke wani saurayi mai kimanin shekaru 13 bayan ya je rajistar layin wayar salula a yankin ’Yan Katako da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa.
Rundunar ’yan sandan Filato ce ta yi wa manema labarai holen saurayin mai suna Umar Hashim tare da wasu mutum shida da ake zargi da garkuwa da kuma kisan wani mai suna Tasiu Abdullahi a ranar 20 ga watan Disamba.
Sai dai da yake yi wa manema labarai jawabi, Hashim ya bayyana cewa jami’an tsaron har gida suka je suka kama shi da cewa an yi amfani da lambar wayarsa wajen karɓar kuɗin fansar mutumin da aka kashe, wato Tasiu Abdullahi.
Hashim ya bayyana cewa tun a ranar 12 ga watan Disamba ya je sayen sabon layin wayar a wurin wani mai suna Usman Abdullahi kuma ya nemi a yi masa rajistarsa.
Sai dai mai rajistar layin ya nemi ya dawo wani lokacin saboda rashin sabis tare da neman ya taho da shaidar ɗan ƙasa ta NIN ta wani ɗan uwansa la’akari da ƙarancin shekarunsa.
“Hashim ya ce, “na dawo na ɗauki shaidar NIN ɗin yayana na koma wurin rajistar layin.
“Sai dai mai rajistar layin ya shaida min ana kan aikin nawa sannan ya aike ni sayen katin waya.
“Bayan na dawo ya [mai rajistar] ce min an kammala aiki kuma ya ba ni layin da aka yi min rajistar na kama gaba na.
“Ba ni da wata masaniyar cewa an yi amfani da layin nawa wajen neman kuɗin fansa kamar yadda jami’an tsaron suke iƙirari.”
A nasa jawabin, mai rajistar layin, Usman Abdullahi, ya ce yaron ya sayi sabon layin ne a wurinsa amma ya bai wa wasu abokansa layin an kammala rajistar.
Sai dai Abdullahi ya ce ba shi da masaniyar abin da abokan suka da layin da suka karɓa kafin dawo wa yaron kayansa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Jihar Filato Rajistar Layi rajistar layin mai rajistar
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya ba ni riƙon Ribas don wanzar da zaman lafiya — Ibas
Shugaban Riƙo na Jihar Ribas, Ibok Ibas, ya ce Shugaba Bola Tinubu, ya naɗa shi ne domin dawo da zaman lafiya a jihar, wadda ke fama da rikicin siyasa.
Da yake jawabi a wani shirin talabijin a daren Alhamis a Fatakwal, Ibas ya bayyana naɗin nasa a matsayin matakin da ya dace don kawo ƙarshen rikicin siyasa da ya ɗauki kusan shekaru biyu.
Farashin fetur na iya tashi bayan Dangote ya daina sayar da mai a Naira Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na RamadanYa ce rikicin ya hana ci gaban gwamnati, tare da haifar da matsalar tsaro da koma bayan tattalin arziƙi a jihar.
“A matsayina na ɗan yankin Neja Delta, na fahimci damuwar mutanenmu. Rashin tabbas a Jihar Ribas ya shafi iyalai, ’yan kasuwa da rayuwar yau da kullum.
“Naɗin da aka yi min ba na siyasa ba ne, sai dai don dawo da doka da oda, tare da tabbatar da cewa mutanenmu suna rayuwa cikin kwanciyar hankali.”
Ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa babban aikinsa shi ne dawo da zaman lafiya, tabbatar da bin doka da oda, tare da samar da yanayin da zai ba da damar ci gaban gwamnati da bunƙasa tattalin arziƙi.
“Ba aikin mutum ɗaya ba ne. Dole ne al’ummar Ribas su haɗa kai, dattawa, sarakunan gargajiya, ’yan siyasa, ’yan kasuwa, matasa da ƙungiyoyin fararen hula.
“Na zo a matsayin wanda zai hidimta wa jihar, wanda ke da nauyin dawo da zaman lafiya da tsari, domin Jihar Ribas ta dawo da matsayinta na cibiyar arziƙin man fetur a Najeriya.”
Ibas, ya gargaɗi ’yan jihar da su guji tashin hankali da aikata laifuka, inda ya bayyana cewa gwamnati ba za ta yarda da duk wani yunƙuri na kawo ruɗani ba.
Sai dai ya tabbatar da cewa zai mutunta haƙƙoƙin ’yan ƙasa tare da bin doka.
Ya buƙaci jama’a da su haɗa kai don girmama juna da samar da zaman lafiya a jihar.