Aminiya:
2025-02-21@14:35:31 GMT

Garkuwa da Mutane: An kama ɗan shekara 13 a wurin rajistar layin waya

Published: 12th, February 2025 GMT

An cafke wani saurayi mai kimanin shekaru 13 bayan ya je rajistar layin wayar salula a yankin ’Yan Katako da ke Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa.

Rundunar ’yan sandan Filato ce ta yi wa manema labarai holen saurayin mai suna Umar Hashim tare da wasu mutum shida da ake zargi da garkuwa da kuma kisan wani mai suna Tasiu Abdullahi a ranar 20 ga watan Disamba.

DAGA LARABA: Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar Hausa An harbe ’yan sanda biyu a Yobe

Sai dai da yake yi wa manema labarai jawabi, Hashim ya bayyana cewa jami’an tsaron har gida suka je suka kama shi da cewa an yi amfani da lambar wayarsa wajen karɓar kuɗin fansar mutumin da aka kashe, wato Tasiu Abdullahi.

Hashim ya bayyana cewa tun a ranar 12 ga watan Disamba ya je sayen sabon layin wayar a wurin wani mai suna Usman Abdullahi kuma ya nemi a yi masa rajistarsa.

Sai dai mai rajistar layin ya nemi ya dawo wani lokacin saboda rashin sabis tare da neman ya taho da shaidar ɗan ƙasa ta NIN ta wani ɗan uwansa la’akari da ƙarancin shekarunsa.

“Hashim ya ce, “na dawo na ɗauki shaidar NIN ɗin yayana na koma wurin rajistar layin.

“Sai dai mai rajistar layin ya shaida min ana kan aikin nawa sannan ya aike ni sayen katin waya.

“Bayan na dawo ya [mai rajistar] ce min an kammala aiki kuma ya ba ni layin da aka yi min rajistar na kama gaba na.

“Ba ni da wata masaniyar cewa an yi amfani da layin nawa wajen neman kuɗin fansa kamar yadda jami’an tsaron suke iƙirari.”

A nasa jawabin, mai rajistar layin, Usman Abdullahi, ya ce yaron ya sayi sabon layin ne a wurinsa amma ya bai wa wasu abokansa layin an kammala rajistar.

Sai dai Abdullahi ya ce ba shi da masaniyar abin da abokan suka da layin da suka karɓa kafin dawo wa yaron kayansa.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Jihar Filato Rajistar Layi rajistar layin mai rajistar

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram

Majalisar Wakilai ta kafa kwamiti na musamman da zai binciki zargin da ake yi wa Hukumar Bayar da Agaji ta Ƙasa da Ƙasa ta Amurka (USAID), da tallafa wa Boko Haram.

An yanke wannan hukunci ne bayan ɗan majalisa, Inuwa Garba, ya gabatar da buƙatar gaggawa a zaman majalisar na ranar Alhamis.

’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina

Garba, ya nuna damuwa game da kalaman da ɗan majalisar dokokin Amurka, Scott Perry, ya yi kwanan nan, inda ya zargi USAID da bai wa ƙungiyoyin ’yan ta’adda, ciki har da Boko Haram tallafi.

Ya jaddada cewa Boko Haram ta haddasa babbar matsalar tsaro a Najeriya sama da shekara 10.

“Scott Perry ya yi wannan iƙirari a wani zaman majalisar dokokin Amurka, inda ya ce ana kashe sama da dala miliyan 697 duk shekara, kuma kai-tsaye ga ƙungiyoyi irin su ISIS, Al-Qaeda, da Boko Haram ne suke amfana,” in ji Garba.

“Boko Haram na da babbar maɓoya a Arewacin Najeriya, don haka akwai yiyuwar sun amfana da wannan tallafi.

“Idan zargin ya kasance gaskiya, hakan babbar barazana ce ga tsaron ƙasa da na duniya baki ɗaya,” in ji shi.

Bayan tattaunawa tsakanin ’yan majalisar, Kakakin Majalisar ya kafa kwamitin bincike na musamman don yin duba a kan lamarin.

Ana sa ran kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin makonni biyu masu zuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno
  • Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)
  • Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Kashe Mutane Fiye Da 400 A Yankin Al-Qatana Da Ke Jihar White Nile Ta Sudan
  • Trump Ya Danganta Zelensky Da Dan Mulkin Kama Karya
  • Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
  • Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Kasuwar Zamfara
  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri