Saudiyya Ta Sake Jaddada Rashin Amincewarta Da Korar Falasdinawa Daga Zirin Gaza
Published: 12th, February 2025 GMT
Kasar Saudiyya ta jaddada matsayinta na yin watsi da kalaman masu tsattsauran ra’ayin sahayoniyyanci game da korar Falasdinawa daga muhallinsu
Saudiyya ta jaddada cewa: Tana yi watsi da kalaman masu tsattsauran ra’ayin sahayoniyyanci game da neman tilastawa al’ummar Falasdinu yin hijira daga yankunansu, kuma ta nuna cewa ba za a samu dawwamammen zaman lafiya ba sai dai ta hanyar amincewa da tsarin zaman lafiya da zai kai ga samar da kasashe biyu na Falasdinawa dana yahudawan sahayoniyya.
Hakan ya zo ne a yayin taron majalisar ministocin Saudiyya da yarima mai jiran gado kuma fira ministan kasar Mohammed bin Salman ya jagoranta, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Saudiyya SPA ya ruwaito.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na SPA cewa: Majalisar zartaswar kasar Saudiyya ta tattauna batutuwan da suka shafi yankin Gabas ta Tsakiya da ma kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Saudiyya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum
A Sudan bayan sake karbe fadar shugaban kasa da ke birnin Khartoum, sojojin kasar sun ci gaba da kai farmaki a babban birnin kasar a ranar Asabar, inda suka sake karbe iko da wasu gine-gine, ciki har da babban bankin kasa da hedkwatar hukumar leken asiri da kuma gidan adana kayan tarihi na kasar.
Ana kallon wannan a matsayin nasarorin ga Janar al-Burhan a babban birnin kasar, wanda rikicin cikin gida ya rutsa da shi na tsawon shekaru biyu.
A wannan Asabar, kakakin rundunar sojojin kasar, Janar Nabil Abdullah, ya sanar a cikin wata sanarwa cewa sojojin na ci gaba da samun nasara a birnin Khartoum, Ya kuma ce sojojin sun “kore daruruwan ‘yan bindiga.
A sa’i daya kuma, ana ci gaba da gwabza fada a yankin Darfur, wanda kusan yana karkashin ikon dakarun RSF.
A cewar masu fafutukar kare hakkin jama’a, akalla fararen hula 45 ne aka kashe a ranar Alhamis a wani harin da dakarun sa kai suka kai a garin Al-Malha da ke arewacin Darfur.
Sojojin sun yi ikirarin cewa sun yi wa garin kawanya tare da kashe makiya sama da 380.