Aminiya:
2025-02-20@08:50:50 GMT

Dokokin gyaran haraji sun tsallake karatu na biyu a majalisa

Published: 12th, February 2025 GMT

Dokokin Gyaran Haraji sun tsallake karatu na biyu a Majalisar Wakilai, bayan tafka muhawara mai zafi a tsakanin ’yan majalisar.

Tun da farko, an gabatar da ƙudirorin guda huɗu wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aike wa majalisar, amma an haɗe su zuwa guda ɗaya domin sauƙaƙa nazari a kansu.

An yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga a Kaduna Ɗan majalisar Kebbi ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC

Jagoran majalisar, Farfesa Julius Ihonvbere ne, ya jagoranci tattaunawar, inda ya jaddada buƙatar sauta tsarin harajin Najeriya.

Ya ce dokokin za su sauƙaƙa biyan haraji, cire harajin kayayyakin buƙatu na yau da kullum kamar abinci da kiwon lafiya, tare da samar da rangwame ga ma’aikata masu ƙaramin ƙarfi.

Yawancin ’yan majalisar sun goyi bayan ƙudirin, inda suka ce hakan zai ƙara wa gwamnati kuɗin shiga tare da bunƙasa tattalin arziƙi ƙasa.

Sai dai wasu, kamar ɗan majalisa Sada Soli, sun nuna damuwa kan wasu sassa da ba a fayyace su ba a ƙudurorin, waɗanda ka iya haifar da matsaloli a nan gaba.

Duk da haka, bayan tattaunawa mai zurfi, majalisar ta amince da ƙudirin a karatu na biyu ta hanyar kaɗa ƙuri’a.

Mataki na gaba shi ne miƙa ƙudirin ga kwamitocin majalisar domin ƙara yin nazari, tare da gyara matsalolin da ke tattare da ƙudirorin.

Idan aka amince da shi, za a gabatar da shi a karatu na ƙarshe kafin ya zama doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan majalisa Dokokin Gyaran Haraji Majalisar Wakilai Muhawara

এছাড়াও পড়ুন:

Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro a Kano

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaron al’umma ta Jihar Kano mai suna ‘Kano State Security Neighborhood Watch.’

Gwamnan ya sanya hannu kan dokar ne tare da wasu ƙarin dokokin guda biyu, waɗanda suka haɗa da dokar gyara hukumar sufuri ta jihar da kuma wadda ta kafa cibiyar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta jihar.

Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi Gubar harsashi ta jikkata mutane dama a Zamfara

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature ya fitar ta ce gwamnan ya amince da dokokin ne a zaman majalisar zartarwar jihar na 25 da ya gudana a fadar gwamnatin jihar.

Hakan na zuwa ne bayan dokar samar da rundunar tsaron ta bi matakan da suka kamata a majalisar dokokin jihar.

Kano dai na fama da matsaloli irin na rikice-rikicen dabanci da ƙwacen waya, lamarin da ya yi sanadiyar ajalin mutane da dama.

Me Abba ya ce?

A jawabinsa bayan rarraba hannu dokokin, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ganin an samu ribar dimokuraɗiyya da kuma bunƙasa tattalin arzikin jihar cikin ƙanƙanin lokaci.

Ya kuma jaddada cewa gwamnati ta tsaya tsayin daka a ƙoƙarinta na ɓullo tare da aiwatar da manufofi da tsare-tsare da nufin inganta rayuwar al’ummar Jihar Kano.

Gwamna Yusuf ya bayyana jin daɗinsa dangane da irin goyon baya da haɗin kai da jama’a ke ba su, inda ya buƙaci da su ci gaba da gudanar da ayyukansu domin cimma manufofin gwamnatin.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Ta Amince Da Biyan Bashin Albashin Ma’aikatan Tsaftar Muhalli 2,369
  • Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane
  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri
  • Majalisa ta tsayar da ranar sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin Dokar Haraji
  • Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro ta Kano
  • Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro a Kano
  • Da Muguwar Rawa, Gwamma Kin Tashi
  • AU Ta Zabi Sabbin Shugabanni Ana Tsaka Da Tashe-tashen Hankula A Nahiyar
  • Yadda Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa Ta Gudanar Da Tantance Sabbin Kwamishinoni
  • Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe