Yadda na ƙi karɓar cin hancin N5bn a gwamnatin Tinubu – Tsohon Hadimi
Published: 12th, February 2025 GMT
Tsohon Hadimin Shugaban Ƙasa a fannin Ƙimar Ƙasa da Zamantakewa, Fela Durotoye, ya bayyana yadda ya ƙi karɓar tayin cin hancin Naira biliyan biyar yayin da yake aiki a Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
Yayin da yake jawabi a wani taro a Abuja, Durotoye ya ce wani jami’i da ya ce shi limamin coci ne, ya matsa masa lamba domin ya ƙara farashin wani shirin horo da gwamnati ta shirya.
Ya bayyana cewa tawagarsa ta ƙiyasta kuɗin aikin zuwa Naira biliyan 1.3, amma bayan kwana uku, aka ce masa ya gabatar da takardar lissafi zuwa Naira biliyan biyar.
“Sun ce kuɗin da na nema ya yi kaɗan, sun ce za su ƙara shi zuwa Naira biliyan biyu.
“Daga nan ne suka buƙaci na ƙara lissafin zuwa Naira biliyan biyar,” in ji shi.
Lokacin da ya tambayi dalilin ƙarin kuɗin, sai jami’in ya ce masa kada ya damu.
“Ya ce min, ‘Ba wani laifi a ciki. Ka yi wa Najeriya hidima sosai, yanzu lokaci ya yi da Najeriya za ta saka maka da alheri,’” in ji Durotoye.
Ya ce ya ƙi yarda da tayin, kuma don guje wa damunsa, sai ya kashe wayarsa.
Watanni kaɗan bayan haka, ya samu labarin cewa an kama wasu jami’an gwamnati da suka wawure Naira miliyan 426 daga kuɗin wani shirin horo da aka shirya.
Durotoye, ya jaddada cewa gaskiya da ɗa’a ne kaɗai za su taimaka wa mutum gujewa cin hanci a Najeriya.
“Idan muna da kyawawan halaye, ba za a samu cin hanci da rashawa a ƙasarmu ba,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnatin zuwa Naira biliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati ta raba wa mata tallafin awakai na N5bn a Katsina
Gwamnatin Katsina ta kashe kimanin Naira biliyan 5.4 domin bai wa mata 3,610 tallafin kiwon awakai.
Gwamna Dikko Umar Radda ne ya bayyana hakan a yayin ƙaddamar da shirin raba tallafin awakan a gundumar Dan-Nakolo da ke Ƙaramar Hukumar Daura ta jihar.
Gwamnati ta kashe N5bn domin bai wa mata tallafin kiwon awakai a Katsina NAJERIYA A YAU: Dalilan Saukar Farashin Kayan Masarufi A KaswanniYa bayyana cewa, a ƙarƙashin shirin, an raba wa mata 3,610 awakai huɗu-huɗu a gundumomi 361 da ke faɗin jihar.
Gwamnan ya bayyana cewa wannan shiri wani ginishiki ne na bunƙasa harkokin noma da kiwo wanda yake da burin ganin Katsina ta zama ja gaba a fannin dogaro da kai a Arewacin Nijeriya da ma ƙasar baki ɗaya.
A cewar Gwamnan, kiwon awakai yana da muhimmanci kuma ɗaya ne daga cikin muradin gwamnantinsa na bunƙasa harkokin noma da kiwo da wadatar abinci sannan kuma abin dogaro da kai ga ƙananan manoma.
A nasa jawabin, mashawarcin gwamnan ma musamman kan harkokin kiwo, Suleiman Yusuf, ya ce bai wa mata tallafin awakai babbar hujja kan yadda gwamnatin ke ƙoƙarin ganin ta rage talauci a tsakanin al’umma.
“Mun ƙaddamar da wannan shiri ne saboda fahimtar da muka yi wa muhimmacin da rawar da mata suke takawa wajen bunƙasar tattalin arziki.
“Saboda haka wannan tallafi aka bai wa matan muna da yaƙinin cewa zai kawo kyakkyawan sauyi a tsakanin al’umma,” in ji Yusuf.