Aminiya:
2025-04-13@09:52:24 GMT

Babban layin wutar lantarki ya faɗi karon farko a 2025

Published: 12th, February 2025 GMT

Babban layin wutar lantarkin Najeriya, ya faɗi a karon farko a shekarar 2025, lamarin da ya haddasa ɗaukewar wuta a wasu sassa.

Wannan matsala ta haifar da katsewar wuta a wasu sassan ƙasar, wanda ya jefa masu amfani da lantarki cikin damuwa.

Na yi nadamar yi wa Tinubu kamfe a 2023 — Ɗan Bilki Kwamanda Yadda na ƙi karɓar cin hancin N5bn a gwamnatin Tinubu – Tsohon Hadimi

Cikin wata sanarwa da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Abuja (AEDC), ya fitar a shafinsa na X, ya bayyana cewa matsalar ta faru ne da misalin ƙarfe 11:34 na safiyar ranar Laraba.

Sai dai AEDC, ya ce ana aiki tare da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da dawo da wutar da zarar an shawo kan matsalar.

Rahotanni, sun nuna cewa yawan wutar lantarki a kan babbar tashar wutar lantarki ta ƙasa (TCN), ya ragu daga megawat 4,064.70 da misalin ƙarfe 11 na safe zuwa megawat 1,222.78 da ƙarfe 12 na rana.

“Muna mai baƙin ciki da sanar da ku cewa wata matsala ta auku a babban layin wuta na ƙasa da misalin ƙarfe 11:34 na safiyar yau, wanda ya haddasa ɗaukewar wuta a yankunanmu.

“Duk da cewa an fara dawo da wuta a hankali, muna tabbatar muku cewa muna aiki tare da hukumomin da suka dace domin maido da wutar gaba ɗaya da zarar an daidaita layin.

“Muna godiya da fahimtarku da haƙurin da kuke yi yayin da muke ƙoƙarin inganta ayyukanmu a gare ku.”

Babban layin lantarki na Najeriya na fuskantar matsalolin faɗuwa akai-akai, musamman a shekarar da ta gabata, inda hakan ke haddasa matsalolin ɗaukewar wuta a faɗin ƙasar.

Wannan na zuwa ne bayan da Najeriya ta fuskanci faɗuwar layin wutar lantarki sau 12 a shekarar 2024.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban Layi damuwa Ɗaukewa Najeriya Wutar Lantarki wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

 

Kazalika, mahalarta taron sun jaddada muhimmancin inganta samar da ayyukan yi, da karfafa tattalin arziki, da kyautata zaman rayuwar ’yan Najeriya, ta hanyar kulla huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare da kasar Sin. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhi: Tattaunawa Zagaye Na Farko Tsakanin Iran Da Amurka A Oman
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Saudiya Tace Shigo Da Agaji Cikin Gaza Bai Da Dangantaka Da Tsagaita Wuta
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing
  • Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji
  • Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa
  • Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma