NHIS: Kotu ta ɗage bayar da belin Farfesa Yusuf zuwa 27 ga Fabrairu
Published: 13th, February 2025 GMT
Wata Babbar Kotu a Abuja, ta ɗage yanke hukunci kan buƙatar bayar da belin Tsohon Shugaban Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, wanda ke fuskantar zargin cin hanci da rashawa.
A ranar Laraba ne, Mai shari’a Chinyere Nwecheonwu, ta bayar da umarnin ci gaba da tsare Yusuf a gidan gyaran hali na Kuje har zuwa ranar 27 ga watan Fabrairu.
A lokacin ne kotun za ta yanke hukunci kan buƙatar bayar da belinsa.
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), na zargin Yusuf da karkatar da kuɗaɗen gwamnati lokacin da yake jagorancin NHIS a shekarar 2016.
Ana zargin ya amince da sayen mota kan kuɗi Naira miliyan 49.2 maimakon Naira miliyan 30 da aka ware a kasafin kuɗi.
Hakazalika, EFCC ta ce Yusuf ya bai wa gidauniyar GK Kanki Foundation kwangilar bayar da horo ta Naira miliyan 10.1ba tare da bin ƙa’ida ba, duk da cewa mutum 45 kaɗai aka horar maimakon 90 da aka bayyana.
Bugu da ƙari, ana tuhumarsa da bai wa kamfanin ɗan uwansa Hassan Yusuf, Lubekh Nigeria Limited kwangilar Naira miliyan 17.5, wadda ita ma aka ce ba bisa ƙa’ida aka yi ta ba.
Yusuf ya musanta duk zarge-zargen da ake yi masa.
A zaman kotun, lauya mai gabatar da ƙara, Francis Usani, ya buƙaci a hana belin Yusuf, inda ya ce bai cika sharuɗan belin da EFCC ta ba shi a baya ba, wanda ya haɗa da wajibcin kai kansa ofishin hukumar sau biyu a kowane mako.
Ya ƙara da cewa Yusuf ya yi fariya da dangantakarsa da masu ruwa da tsaki a siyasa, don haka akwai yiwuwar ya tsere idan aka bayar da belinsa.
Ya kuma bayyana cewa jami’an EFCC sun sha wahala kafin su kama shi tare da gurfanar da shi a kotu.
Sai dai lauyan Yusuf, O.I. Habeeb (SAN), ya roƙi kotu da ta bayar da belinsa, inda ya ce laifukan da ake zargin sa da suna da ikon samun beli bisa doka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Usman Yusuf zargi bayar da belin Naira miliyan
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa
’Yan bindiga sun kashe wasu mazauna ƙauyen Gwargwada da ke Ƙaramar Hukumar Kuje a saboda jinkirin biya musu kuɗin fansa.
Mutanen da aka kashe, sun haɗa da Mohammed Danladi da Nasiru Yusuf, wanɗanda aka sace su ne a ranar Laraba tare da wani makiyayi da wata mata a mahaɗar Gwombe, a kan hanyar Gwargwada zuwa Rubochi.
Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo Rayuka 10 da dukiyar N11bn sun salwanta yayin zanga-zangar tsadar rayuwa a KanoWani ɗan uwan mamatan, Shuaibu Abdullahi, ya shaida wa Aminiya cewa maharan sun nemi iyalan waɗanda lamarin ya shafa su biya wa kowa Naira 500,000 amma Naira 500,000 suka iya tattaraws baki ɗayansu.
“Shugaban maharan ya kira mu ranar Juma’a, muka sanar da shi cewa Naira 500,000 kacal muka samu. Ba mu san cewa tuni sun kashe su ba saboda jinkirin biyan kuɗin fansar ba,” in ji shi.
Abdullahi ya ce bayan haka, ’yan bindigar sun saki makiyayin da matar da suka sace bayan an biya su Naira miliyan uku a maɓoyarsu da ke cikin dajin Kotonkarfe, a Jihar Kogi.
Shugaban yankin Gwargwada, Ugbada Alhaji Hussaini Agabi Mam, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an sace matasan ne a hanyarsu ta dawowa daga Rubochi.
“Abin takaici, an kashe matasan nan biyu saboda kawai danginsu sun yi jinkiri wajen biyan kuɗin fansa,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa ba a samu gawarwakin mamatan ba domin an kai su cikin dajin Kotonkarfe.
“Na samu labarin cewa shugaban Ƙaramar Hukumar Kotonkarfe ya tura maharba da jami’an tsaro don su shiga dajin su nemo gawarwakin, amma har yanzu ba su same su ba,” in ji shi.
Rundunar ’Yan Sandan Babban Birnin Tarayya, ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.