Aminiya:
2025-03-22@13:13:51 GMT

NHIS: Kotu ta ɗage bayar da belin Farfesa Yusuf zuwa 27 ga Fabrairu

Published: 13th, February 2025 GMT

Wata Babbar Kotu a Abuja, ta ɗage yanke hukunci kan buƙatar bayar da belin Tsohon Shugaban Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, wanda ke fuskantar zargin cin hanci da rashawa.

A ranar Laraba ne, Mai shari’a Chinyere Nwecheonwu, ta bayar da umarnin ci gaba da tsare Yusuf a gidan gyaran hali na Kuje har zuwa ranar 27 ga watan Fabrairu.

Sojoji sun doki ’yan sanda kan kama ‘mai laifi’ Fitaccen ɗan siyasa Ahmadu Haruna Zago ya rasu

A lokacin ne kotun za ta yanke hukunci kan buƙatar bayar da belinsa.

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), na zargin Yusuf da karkatar da kuɗaɗen gwamnati lokacin da yake jagorancin NHIS a shekarar 2016.

Ana zargin ya amince da sayen mota kan kuɗi Naira miliyan 49.2 maimakon Naira miliyan 30 da aka ware a kasafin kuɗi.

Hakazalika, EFCC ta ce Yusuf ya bai wa gidauniyar GK Kanki Foundation kwangilar bayar da horo ta Naira miliyan 10.1ba tare da bin ƙa’ida ba, duk da cewa mutum 45 kaɗai aka horar maimakon 90 da aka bayyana.

Bugu da ƙari, ana tuhumarsa da bai wa kamfanin ɗan uwansa Hassan Yusuf, Lubekh Nigeria Limited kwangilar Naira miliyan 17.5, wadda ita ma aka ce ba bisa ƙa’ida aka yi ta ba.

Yusuf ya musanta duk zarge-zargen da ake yi masa.

A zaman kotun, lauya mai gabatar da ƙara, Francis Usani, ya buƙaci a hana belin Yusuf, inda ya ce bai cika sharuɗan belin da EFCC ta ba shi a baya ba, wanda ya haɗa da wajibcin kai kansa ofishin hukumar sau biyu a kowane mako.

Ya ƙara da cewa Yusuf ya yi fariya da dangantakarsa da masu ruwa da tsaki a siyasa, don haka akwai yiwuwar ya tsere idan aka bayar da belinsa.

Ya kuma bayyana cewa jami’an EFCC sun sha wahala kafin su kama shi tare da gurfanar da shi a kotu.

Sai dai lauyan Yusuf, O.I. Habeeb (SAN), ya roƙi kotu da ta bayar da belinsa, inda ya ce laifukan da ake zargin sa da suna da ikon samun beli bisa doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Usman Yusuf zargi bayar da belin Naira miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar

Fadar Shugaban Kasar Nijeriya, ta yi watsi da rahoton baya-bayan nan da kwamitin hulda da kasashen wajen Amurka ya fitar, wanda ya kafa hujja da amincewar majalisar dokokin kasar, na zargin kakaba wa wasu kiristoci takunkumi a kasar.

Mai bai wa shugaban kasa shawara a kan harkokin siyasa, Daniel Bwala, ya bayyana rahoton a matsayin wanda ba shi da tushe da makama, yana mai jaddada cewa; tun bayan lokacin da Shugaba Tinubu ya dare kan kujerar mulki a ranar 29 ga Mayun 2023, al’amuran cin zarafi, musamman ta fuskar addini suka yi matukar ja da baya.

Bwala, ya yi wannan furuci ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, wato na D; yana mai jaddada cewa, gwamnatinsu mai ci yanzu; ta himmatu wajen kokarin daidaita addinai a matsayin abu guda.

“Gwamnatin Bola Tinubu, koda-yaushe na kokarin bai wa addinai muhimmanci na musamman. Tun daga ranar 29 ga Mayun 2023, daidai lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya hau kan karagar mulki, ba a taba samun wasu matsaloli na tsananta wa Kiristoci a ko’ina a fadin wannan kasa ba”, kamar yadda ya rubuta.

Ya jaddada cewa, Nijeriya ta kasance kasa mai dauke da addinai daban-daban, sannan a kowane lokaci gwamnati na kokarin samar da zaman lafiya a tsakanin wadannan addinai.

Martanin da Fadar Shugaban Kasar ta mayar, ya biyo bayan nuna damuwa a kan matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta dauka na amincewa da takunkumin da aka kakaba wa Nijeriya, bisa zargin kashe Kiristoci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Gwamnatin Bauchi Ta Ɗage Hawan Daushe Na Sallar Bana
  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Kotu Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • Gwamna Yusuf Ya Yi Sabbin Nade-Nade A Kano
  • Masarautun Kano Zasu Gudanar da Hawan Daba A Bikin Sallah Karama
  • EFCC Ta Cafke Akanta-janar Na Jihar Bauchi Kan Zargin Badaƙalar Naira Biliyan 70