Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da bibiyar ’yan ta’adda har sai an fatattake su, an ruguza su tare da murƙushe su.

Gwamnan ya miƙa kayan aikin da gwamnatin jihar Zamfara ta samar domin kafa hedikwatar tsaro ta dakarun sojin ‘Operation Safe Corridor’ na jihohin Arewa maso Yamma.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa ‘Operation Safe Corridor’ zai ta tabbatar da canja ƙwaƙwale, haɗe kai magance duk al’amuran da suka shafi ’yan bindiga.

Sanarwar ta ƙara da cewa, an tsara shirin ne a ƙarƙashin Operation Safe Corridor a yankin Arewa maso Gabas, wanda ya yi nasarar sauya ƙwaƙwalen tsoffin mayaƙan Boko Haram tare da gyara tubabbun su.

“Shirin Arewa maso Yamma na neman bayar da tsarin tuba ga mutanen da ke da hannu cikin ayyukan ‘yan bindiga. Wannan yunƙurin zai ƙunshi horar da su wajen sana’o’i, canja musu tunani, da sake musu fasalin aƙida.”

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya ce gwamnatin jihar ta samar da wurin ne a matsayin wani shiri na taimaka wa gwamnatin tarayya wajen magance matsalar ‘yan bindiga da ya addabi Zamfara da Arewa maso Yamma sama da shekaru goma.

“Ina so in sake mayar da alƙawarin da gwamnatinmu ta yi na tallafa wa waɗannan tsare-tsare da sauran dabaru masu inganci da ake amfani da su wajen kai wannan yaƙi zuwa ga ’yan bindigar har sai an fatattake su yadda ya kamata tare da murƙushe su.

“Amma ga waɗanda suka yi niyyar miƙa makamansu ba tare da wani sharaɗi ba da son rai, suna da ‘yancin yin hakan. Kafa Hedikwatar Rundunar Tsaro ta Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma zai ba da dama da masu niyyar tuba tare da gyara musu ɗabi’arsu.

“A kan wannan batu, ina so in miƙa godiyata ga Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Musa, na ganin jihar Zamfara ta cancanci karbar baƙuncin Operation Safe Corridor na 3 a ƙasar nan.

“Ina kuma so in gode wa shugaban kwamitin aiwatar da ayyukan Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma, Manjo Janar EV Onumajoro, wanda kuma shi ne Babban Hafsan Harkokin Tsaro na Hedikwatar Tsaron Nijeriya, da tawagarsa saboda ganin Zamfara ta dace da kafa hedikwatar wannan muhimmin dakaru.

“Daga ƙarshe muna godiya ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, kuma Babban Kwamandan Askarawan Tarayyar Nijeriya, bisa dukkan ƙoƙarinsa da goyon bayansa ga hukumomin tsaro da ke aiki a jihar.

“Abin da ake buƙata shi ne ƙara ƙarfafa nasarorin da aka samu wajen murƙushe ayyukan ’yan bindiga da sauran aikata laifuka. Ina so in tabbatar muku da ƙudurinmu na yin komai don ganin cewa wannan shirin ya yi nasara. A garemu a yau, wannan shi ne haihuwar sabuwar Zamfara mai tsari.

“Da waɗannan ‘yan kalamai, ina so in miƙa wannan cibiyar domin yin aiki a matsayin hedikwatar Operation Safe Corridor na Arewa maso Yamma domin amfanin jihar Zamfara da kuma ƙyaunatacciyar ƙasarmu Nijeriya.”

Tun da farko, Manjo Janar Onumajuru, wanda ya wakilci Babban Hafsan Tsaron Ƙasar, ya yaba wa Gwamna Lawal bisa goyon bayan da yake baiwa sojoji a yaƙin da ake da ’yan bindiga a Zamfara.

“Operation Safe Corridor dakaru ce mai aiki da cikakken tsari. Tana aiki a matsayin hanyar samar da zaman lafiya. Bayan karbar ragamar wannan ginin, za mu ci gaba da haɗa kai da Gwamna da al’ummar Zamfara, waɗanda su ne masu ruwa da tsaki a wannan aiki, domin tabbatar da haɗin kai da samun nasara.

Aminu Dalhatu/Gusau

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lawal Tsaro Zamfara Arewa maso Yamma jihar Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Yi Sabbin Nade-Nade A Kano

A wani gagarumin yunkuri na karfafa harkokin mulki da inganta ayyukan yi, gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da nada wasu mukamai da karin girma.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar.

 

Sabbin canje-canje da suka samo asali ne daga kwararru da matasa, suna ƙarfafa sadaukarwar gwamnati don kyakkyawan tsari, ingantawa.

 

Wadanda aka nada ko kuma aka karawa mukamai daban-daban sune kamar haka.

 

An nada Architect Hauwa Hassan Tudun Wada a matsayin Manajan Darakta na Hukumar Tsare-tsare da Raya Birane ta Kano (KNUPDA). Ita ma’aikaciyar Cibiyar Gine-gine ta Najeriya ce kuma mataimakiyar shugabar masu gine-ginen mata a Najeriya. Kafin wannan nadin, ta yi aiki a matsayin Ƙwararrun a Hukumar Raya Babban Birnin Tarayya Abuja (FCDA). Hauwa ta yi ND, HND, BSc, da MSc a fannin gine-gine a Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, kuma tana cikin mata masu zanen gine-gine na farko daga Kano da suka yi fice a wannan sana’a.

 

An nada Mustapha Muhammad a matsayin babban sakataren yada labarai na gwamna kuma mataimakin kakakin gwamnan. Gogaggen ɗan jarida wanda ya shafe shekaru sama da ashirin yana gogewa, a baya ya yi aiki a matsayin Babban Mai Watsa Labarai a BBC. Yana da digiri na BSc da MSc a harkokin aikin jarida (Mass Communication) kuma a halin yanzu yana karatun digiri na uku a fanni guda. A cikin sabon aikinsa, ana sa ran zai yi aiki a ƙarƙashin Babban Darakta, Watsa Labarai don tallafawa ayyukan watsa labarai da dabarun sadarwa ga gwamnatin Abba Kabir Yusuf.

 

An nada Auwal Lawan Aramposu a matsayin mataimakin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Titunan Kano ta KAROTA. Ya kasance tsohon shugaban karamar hukumar Nasarawa kuma ya taba zama babban mataimaki na musamman (SSA) akan ICT ga tsohon gwamnan jihar Kano.

 

An nada Dr. Tukur Dayyabu Minjibir a matsayin mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin noma. Tsohon Manajan Darakta ne na Kamfanin Samar da Aikin Noma na Kano, kuma Babban Malami a Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya. Dakta Minjibir ya yi digirin digirgir a fannin aikin gona, inda ya kware a kan aikin gona.

 

Baya ga wadannan muhimman mukamai, Gwamna Yusuf ya amince da karin girma ga wasu manyan jami’ai guda biyu.

 

Zulaihat Yusuf Aji ta samu mukamin mataimakiyar Manajan Darakta ta gidan rediyon Kano. Kafin sabon nadin nata, ta yi aiki a matsayin Babbar Mataimakiyar ta Musamman akan Watsa Labarai (1) da Hulda da Jama’a ta Gidan Gwamnati. Gogaggiyar ‘yar jarida, Zulaihat a baya ta yi aiki da Freedom Radio Kano.

 

Injiniya Abduljabbar Nanono ya zama mataimakin Manajan Darakta na KHEDCO. Yana da Digiri na biyu a fannin Makamashi mai sabuntawa kuma a baya ya yi aiki a matsayin Babban Mataimaki na Musamman akan Sabunta Makamashi.

 

Dukkan nade-naden mukamai da mukamai sun fara aiki nan take, wanda ke nuni da kudurin Gwamna Yusuf na samar da ingantacciyar gwamnati, da hada kai, da kuma samun sakamako mai inganci.

 

Yayin da yake taya sabbin wadanda aka nada, gwamnan ya ba su tabbacin goyon bayansa, sannan ya bukace su da su yi aiki tukuru a kan ayyukansu domin bayar da tasu gudummawar ga ci gaban jihar Kano.

 

Saki/ABDULLAHI JALALUDDEEN/KANO

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba Gwamna Bala Ne Ya Soke Hawan Daushe Ba – Masarautar Bauchi Ta Bayyana Gaskiya
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • ’Yan bindiga sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna
  • Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa
  • Sallah: Tinubu Ya Raba Wa ’Yan APC Buhun Shinkafa 7,000 A Zamfara
  • Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai
  • Gwamna Yusuf Ya Yi Sabbin Nade-Nade A Kano
  • Mun Yi Watsi Da Ayyana Dokar Ta-Ɓaci Da Tinubu Ya Yi A Ribas – Shugabannin Adawa
  • Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara
  • Gobara Ta Babbake Wani Shago A Jihar Kwara