Makwabta sun kai karar ma’aurata saboda carar zakaransu
Published: 15th, February 2025 GMT
Wasu magidanta da suka mallaki wani zakara (Ricco) jinsin Bantam daga Bourgoin-Jallieu a sashen Isère na kasar Faransa, sun karɓi sammaci domin bayyana a gaban kotu sakamakon korafin da wani makwabcinsu ya yi game da carar zakaran.
Korafin da suka yi ya hada da, rashin barci saboda karar zakaran yake yi a yayin carar, kamar yadda mai gabatar da ƙara ya ambata, wanda ya gayyaci masu zakara (Ricco) zuwa kotu a watan Janairun 2025.
Mutumin, wanda ya fi son a sakaya sunansa, yana daya daga cikin makwabtan masu ikirarin cewa, carar zakaran ba za a iya jure ta ba da daddare da rana.
Masu wannan zakaran mai shekaru 5 a koyaushe suna musanta wadannan ikirari, inda suka kafe a kan cewa, zakaran yana da tsarin sarrafa kansa wanda ya tsara yin carar daga karfe 8:30 na safe a lokacin hunturu da karfe 9:00 na safe a lokacin rani.
Sun dage cewa, zakara ya kan yi cara kamar sau 15 a cikin mintuna 15 da safe, sannan sai ya kara yin cara da rana.
“Akwai tsarin da yake bi, wanda yake nuna cewa, yana rufe yin carar daga karfe 8 na dare. Kuma yana farawa da karfe 9 na safe a lokacin rani, 8:30 na safe a cikin hunturu,” in ji Franck, mamallakin zakaran (Ricco).
Da muka kawo zakarar, sai muka cewa kanmu don kada ya damu makwabtanmu, sai muka tabbatar an bude kofar kejinsa daga karfe 8:30. Sai muka yanke shawarar buɗe shi da karfe 9:00 na safe.
“Mun fahimci cewa, lokacin sanyi, kaji ba sa yin kwai don suna bukatar haske.
“Don haka a lokacin sanyi, muna bude shi da karfe 8:30, kuma a lokacin rani muna bude shi daga karfe 9:00 na safe.”
Ma’auratan sun koma garin Bourgoin-Jallieu da ke birnin shekaru 25 da suka gabata don yin rayuwa mai sauki kuma, inda suka yi mamakin matakin shari’a da makwabcinsu ya dauka.
Da farko sun yi kokarin sasantawa ta hanyar tattaunawa da makwabtan, amma hakan bai yuwu ba, kuma makwabcin ma’auratan ya yanke shawarar kai su kotu.
Franck ya yi ikirarin cewa, ya yi magana da kowanne daga cikin makwabtansu, kuma babu dayansu da ke da matsala da carar zakaran.
“Mun je wajen dukkan makwabtan, mun san wasu daga cikin matsalolinsu saboda mun zauna a nan tsawon shekaru 25,” in ji Franck.
“Mun tambaye su ko zakara yana damun su. Duk wadanda muka tuntuba cewa zakara ya dame su. Sai a samu akasin haka, suna son su ji carar zakara.”
A gefe guda, wacce ta shigar da karar, wanda ta koma Bourgoin Jallieu a cikin 2021, ta kafe a kan cewa carar da zakaran ke yi tana hana ta jin dadin lambunta da yin barci mai kyau, kuma suna son yanayin ya canza.
Rikicin shari’ar game da carar zakarar ya mayar da hankali ne kan dokar Faransa ta Janairu 29, 2021.
A gefe guda, masu zakaran sun yi imanin cewa, suna zaune a cikin yankin da ya kasance yankunan karkara ce, yayin da makwabcinsu ya yi imanin cewa, gundumar Boussieu ba ta kasance a cikin karkara ba.
A wannan shekarar ce alkali zai yanke hukunci kan wannan batu. Abin farin ciki ga zakara Ricco, yana da goyon bayan shafukan sada zumunta na zamani.
An kirkiro masa wani shafi a Fesbuk na goyon bayansa, inda mutane ke karfafa masa gwiwa ya ci gaba da yin cara da kuma gayyatar masu sukar zakaran da su yi kaura idan ba sa son “cararsa”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Carar Zakara Faransa Zakara carar zakaran carar zakara
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda na yi wa budurwar da muka haɗu a Facebook gunduwa-gunduwa —Matashi
Wani matashi da aka kama kan yin gunduwa-gunduwa da budurwarsa da suka haɗu a Facebook bayan ta je ɗakinsa ya bayyana dalilinsa na aikata hakan.
Matashin mai shekaru 29 da ke iƙirarin malumtar addini ya amsa a wurin ’yan sanda masu bincike cewa shi ne ya yi wa gawar budurwar tasa gunduwa-gunduwa.
Ya shaida musu cewa a Facebook ya haɗu da ita, inda daga bisani ta ziyarci ɗakinsa a unguwar Olunlade a garin Ilori, bayan ta je wani biki.
Sai dai ya musanta zargin da ake masa na kashe ɗalibar mai suna Hafsah Yetunde Bello domin yin tsafi.
Jirgin soji ya kashe fararen hula a Katsina Malaman addini sun yi wa ’yan siyasa juyin mulki —Sule Lamiɗo Ku tona asirin ’yan tsubbu —Sarkin Ilori ga malaman addiniA cikin bidiyon tambayoyin da ’yan sanda ke wa matashin mai suna Abdulraham Bello, ya ce bayan zuwan budurwar tasa ne ya je ya sayo mata abinci, bayan ta bayyana masa cewa tana jin yunwa.
Ya shaida wa masu binciken nasa cewa bayan ya dawo daga sayo abincin ne ya iske ta tana shassheka a ɗakin.
“Ba a jima ba sai ta mutu. Ni kuma na tsotsa, babu wanda zan iya zuwa gaya wa ya taimaka min, shi ne ne sassara gawarta na yi mata gunduwa-gunduwa na je na jefar a wata bola a unguwar.
“A rikice nake, ban san abin da zan yi ba, ko tunanin wata hanya ta daban. Amma ban taɓa yin haka ba, wannan ne karon farko,” in ji matashin a ofishin ’yan sanda.
A cikin bidiyon da ya yi jawabin nasa cikin harshen Yarbanci ya bayyana cewa a halin yanzu yana neman gurbin karatu ne a Jami’ar Jihar Kwara (KWASU), Malete.
Mamaciyar dai ɗalibar aikin ƙarshe ce a Kwalejin Koyarwa ta Jihar Kwara.