Leadership News Hausa:
2025-03-23@03:21:31 GMT

Nazari A Kan Noman Agwaluma

Published: 15th, February 2025 GMT

Nazari A Kan Noman Agwaluma

Har ila yau, nau’in Agwaluma na agbalumo ko kuma na Udara, na bukatar yi masa ban ruwa sosai, musamman don ya yi saurin nuna a cikin kasar noman da aka shuka shi.

Bugu da kari, idan manomi zai sayo Irin nomansa, ya tabbatar da ya sayo a gurin da aka fi sani, musamman don ya samu ingantacce kuma mai lafiya.

Ba  Ta Kariya Daga Kamuwa Da kwari Ko Sauran Cututtukan Da Ke Harbin Amfanin Gona:

Ana bukatar manomi ya tabbatar da yana ba ta kariya daga harbin kwari ko cututtukan da ke yi mata illa bayan ana shuka ta, domin irin wadannan cututtukan ko kwarin na iya hana Irinta da aka shuka ruba a cikin kasar noman da aka shuka Irin.

Zuwa Tsawon Wane Lokaci Agwaluma Ke Kammala Girma?

Bayan an shuka Agwaluma, musamman Gona na fara fitar da ‘ya’yanta ne daga shekara biyar zuwa 10, inda kuma ake saran saiwar  jikinta, domin adana wa ta fi bukatar yanayin da ya kai ma’unin yanayi daga 60 zuwa 70.

Har ila yau, wasu sun yi hasashen cewa, ba za a iya yin noman Agwaluma a Nijeriya ba, amma maganar ba haka take ba; domin ana iya yin nomanta kuma ta yi kyau sosai har dimbin wacce za a yi hada-hadar kasuwancinta abin da kawai ake bukata shi ne, mayar da hankali kan shuka ta da aka yi da nuna kwarin gwiwa da kuma ba ta kulawar da ta dace.

Abubuwan Da Ya Kamata A Tanada Na Noman Agwaluma Don Samun Riba A Nijeriya

Samar Da Kyakkyawan Tsari:

Kafin ka fara yin nomanta, ka tabbatar ka tsara  yadda noman nata zai kasance, musamman domin kaucewa yin asara bayan ka  zuba jarinka a ciki.

Gyaran Gonar Shuka Ta:

Kafin ka shuka Irinta, ana bukatar ka tabbatar da kasar noman nata mai kyau ce.

Zabo Nau’in Da Ya Dace:

Na bukatar ka zabo daga cikin nau’ukanta biyu, wato na  Udara ko kuma na Agbalumo, inda ake iya gano su ta hanyar girmansu.

Amfanin na kai wa tsawon shekara takwas kafin ta kammala girma, inda kuma aka kara habaka nau’insa wanda zai iya girma bayan shekara uku.

Yadda Ake Girbe Agwaluma:

Akasari, ana  girbe ta ne a watan Disamba, sai dai a wannan lokaci, ba ta yin dadi sosai; saboda haka, ana so a bar ta a gonar da aka shuka ta har wani ruwan saman ya kara dukan ta kafin a girbe ta, inda ake  yi mata girbin bayan Ganyen ta ya rikide zuwa ruwan dorawa.

Tsara Dabarun Hada-Hadar Kasuwancinta:

Bayan an shuka ta ta girma, za a iya kai ta kasuwa don sayarwa, domin ana nuna ci gaba da batan ta a kasuwa ganin cewa, ana yawan yin amfani da ita. Haka kuma manomi, zai iya wallafa tallan ta a kafar yanar gizo, don masu bukata su gani su kuma saya.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nazari

এছাড়াও পড়ুন:

Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum

Gwamnatin Jihar Borno, ta ɗauki matakin hukunta wasu ma’aurata, Mamman Sheriff da matarsa, da aka kama suna cin zarafin wata yarinya a unguwar Pompomari Bypass da ke Maiduguri.

Bayan bayyanar faifan bidiyon da ya nuna ma’auratan suna dukan yarinyar, mutane da dama sun yi tir da abin a shafukan sada zumunta.

Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia

Wannan ya sa Hukumar Tsaron Sibil Difens (NSCDC) ta cafke su nan take.

Gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum, ya tabbatar da cewa gwamnati ba za ta musu sassauci ba.

Ya ce ma’aikatun shari’a, ilimi, da harkokin mata sun haɗa kai domin ganin an hukunta waɗanda suka aikata laifi.

Yarinyar, wacce ɗaliba ce, ta shiga harabar gidan ma’auratan domin tsinkar mangwaro bayan tashi daga makaranta, inda suka yi mata dukan kawo wuƙa.

A halin yanzu tana kwance a asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), inda Dokta Lawan Bukar Alhaji ya ɗauki nauyin jinyarta.

Gwamnatin Borno ta kuma tallafa wa iyayen yarinyar da kayan agaji, abinci, da kuɗi.

Iyayenta da sauran jama’a sun yaba wa gwamnatin kan matakin da ta ɗauka na kare haƙƙin yarinyar.

Gwamnati ta jaddada cewa duk wanda aka kama da cin zarafin yara ba zai tsira daga hukunci ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari
  • Shirin Fim Kan Cikar Nijeriya Shekaru 25 A Kan Turbar Dimokuradiyya: Tasiri Da Muhimmanci
  • Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum
  • Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Karfafa Cinikayya Da Ketare Tare Da Fadada Bude Kofa
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum
  • Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
  • Jakadan Amurka Ya Ziyarci Sarkin Zazzau Domin Karfafa Alakar Amurka Da Najeriya