Aminiya:
2025-03-23@03:28:22 GMT

IPAC ta amince da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Katsina

Published: 17th, February 2025 GMT

Ƙungiyar Gamayyar Jam’iyyun Siyasa ta Ƙasa (IPAC), reshen Jihar Katsina, ta bayyana amincewarta da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025.

Shugaban ƙungiyar, Alhaji Laminu Lawal Boyi, ya bayyana cewa IPAC ta gamsu da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana, tare da bai wa dukkanin jam’iyyun siyasa damar shiga zaɓen.

Fusatattun matasa sun ƙone ofishin ’yan sanda a Ondo NAFDAC ta gano wajen da ake sabunta magungunan da suka lalalce a Abiya

“Baya ga shugabancina a IPAC, ni kuma shugaban jam’iyyar Accord ne, wacce ta shiga zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 34 da kujerun kansiloli 361 a faɗin jihar.

“A matsayina na ɗan takara kuma mai ruwa da tsaki, na gamsu da yadda aka gudanar da zaɓen,” in ji shi.

Da yake yi wa manema labarai jawabi a ofishin IPAC da ke Kofar Durbi, a cikin garin Katsina, tare da wasu jiga-jigan ƙungiyar, Alhaji Laminu ya jaddada cewa a kowane zaɓe dole ne a samu wanda zai yi nasara da kuma wanda ba zai yi ba.

Ya yi kira ga waɗanda ba su yi nasara ba da su karɓi ƙaddara tare da duba gaba, domin siyasa ba ta ƙarewa.

Haka kuma ya shawarci waɗanda suka yi nasara da su fahimci cewa nasarar ba daga ƙarfinsu ko dabara ta fito ba, sai dai hukuncin Allah ne.

Don haka, ya buƙace su da su sauke nauyin da ke kansu cikin adalci, ba tare da nuna bambancin jam’iyya ba, domin yanzu lokaci ne na haɗin kai da ci gaban al’umma gaba ɗaya.

Alhaji Laminu ya ƙara da cewa, “Yanzu siyasa ta wuce, lokaci ne na aiki da tabbatar da ci gaban jama’a.

“Waɗanda suka samu nasara su yi mulki da adalci, su guji nuna bambanci, domin yanzu dukkanin al’umma na kallonsu a matsayin shugabanninsu, ba wai na jam’iyyarsu kaɗai ba.”

Shugaban ya yaba wa dukkanin ’yan takara da jam’iyyun siyasa da suka shiga zaɓen, tare da gode wa hukumomin da suka shirya zaɓen bisa ƙoƙarin da suka yi wajen tabbatar da gudanar da shi cikin zaman lafiya da lumana.

Ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa shugabanni goyon baya domin ci gaban Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Amincewa gamayya Ƙungiya

এছাড়াও পড়ুন:

Falasdinawa 80,000 ne suka halarci sallar Juma’a a mako na uku na Ramadan a masallacin Al-Aqsa

An gudanar da Sallar Juma’a a mako na uku na watan Ramadan a Masallacin Al-Aqsa, duk kuwa da tsauraran takunkumin da gwamnatin yahudawan sahyoniya ta dauka, tare da halartar Palasdinawa 80,000.

Kamfanin dillancin labaran Al-Naba y bayar da rahoton  cewa, dubun dubatar Falasdinawa ne suka gudanar da sallar Juma’a ta uku na watan Ramadan a masallacin Al-Aqsa, duk da matakai na kawo cikas da sojojin mamaya na Haramtacciyar Kasar Isra’ila suka dauka da kuma yanayin sanyi da ruwan sama a birnin Kudus.

Hukumar kula da lamurran addinin Musulunci a birnin Kudus ta bayar da bayanin cewa, masallata 80,000 ne suka gudanar da sallar Juma’a ta uku na watan Ramadan a masallacin Al-Aqsa.

Sheikh Khalid Abu Juma, limamin masallacin Al-Aqsa, ya ce a cikin hudubar sallar: “Watan Ramadan yana kawo azama da azama a cikinmu; Musulmai sun bar al’adun da suka saba a cikin saurin watanni; Suna nisantar da kansu daga al’adun da suka saba, tare da karfafa ayyukan tsarkeke ruhi da kusanci ga Allah.

Abu Juma ya jaddada cewa azumi yana karfafa nufi da kuma inganta azama, ya kara da cewa: Imani da azama suna da alaka da ruhi.

Ya ce: Yunkurin da makiya suke yi na rusa zaman lafiya da kwanciyar hankali ya sabawa koyarwar addinin muslunci da dukkanin addinai da aka saukar daga sama.

Sannan kuma ya yi ishara da abin da ke faruwa a Gaza, yana bayyana shi a matsayin aiwatar da wani mummunan kudiri na makiya a kan al’ummar musulmi na Gaza da ma Falastinu baki daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa
  • An gudanar da gagarumar zanga-zangar nuna goyon bayan Falastinu a kasar Jordan
  • Falasdinawa 80,000 ne suka halarci sallar Juma’a a mako na uku na Ramadan a masallacin Al-Aqsa
  • Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina
  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu A Tarayyar Najeriya Ya Bada Umurnin A Gudanar Da Bincike Kan hatsarin Daren Laraban da Ta Gabata A Abuja
  • Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
  • An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Taimakon NAMA Don Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Cikin Nasara 
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara