Aminiya:
2025-02-20@08:58:29 GMT

IPAC ta amince da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Katsina

Published: 17th, February 2025 GMT

Ƙungiyar Gamayyar Jam’iyyun Siyasa ta Ƙasa (IPAC), reshen Jihar Katsina, ta bayyana amincewarta da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025.

Shugaban ƙungiyar, Alhaji Laminu Lawal Boyi, ya bayyana cewa IPAC ta gamsu da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana, tare da bai wa dukkanin jam’iyyun siyasa damar shiga zaɓen.

Fusatattun matasa sun ƙone ofishin ’yan sanda a Ondo NAFDAC ta gano wajen da ake sabunta magungunan da suka lalalce a Abiya

“Baya ga shugabancina a IPAC, ni kuma shugaban jam’iyyar Accord ne, wacce ta shiga zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 34 da kujerun kansiloli 361 a faɗin jihar.

“A matsayina na ɗan takara kuma mai ruwa da tsaki, na gamsu da yadda aka gudanar da zaɓen,” in ji shi.

Da yake yi wa manema labarai jawabi a ofishin IPAC da ke Kofar Durbi, a cikin garin Katsina, tare da wasu jiga-jigan ƙungiyar, Alhaji Laminu ya jaddada cewa a kowane zaɓe dole ne a samu wanda zai yi nasara da kuma wanda ba zai yi ba.

Ya yi kira ga waɗanda ba su yi nasara ba da su karɓi ƙaddara tare da duba gaba, domin siyasa ba ta ƙarewa.

Haka kuma ya shawarci waɗanda suka yi nasara da su fahimci cewa nasarar ba daga ƙarfinsu ko dabara ta fito ba, sai dai hukuncin Allah ne.

Don haka, ya buƙace su da su sauke nauyin da ke kansu cikin adalci, ba tare da nuna bambancin jam’iyya ba, domin yanzu lokaci ne na haɗin kai da ci gaban al’umma gaba ɗaya.

Alhaji Laminu ya ƙara da cewa, “Yanzu siyasa ta wuce, lokaci ne na aiki da tabbatar da ci gaban jama’a.

“Waɗanda suka samu nasara su yi mulki da adalci, su guji nuna bambanci, domin yanzu dukkanin al’umma na kallonsu a matsayin shugabanninsu, ba wai na jam’iyyarsu kaɗai ba.”

Shugaban ya yaba wa dukkanin ’yan takara da jam’iyyun siyasa da suka shiga zaɓen, tare da gode wa hukumomin da suka shirya zaɓen bisa ƙoƙarin da suka yi wajen tabbatar da gudanar da shi cikin zaman lafiya da lumana.

Ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa shugabanni goyon baya domin ci gaban Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Amincewa gamayya Ƙungiya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Ci-gaban Da Hukumomin Raya Shiyyoyi Za Su Samar

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A kwanakin baya ne dai Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙirƙiro sababbin hukumomin raya shiyyoyin ƙasar nan da nufin kawo musu ci-gaba.

Gabanin ƙirƙirar waɗannan hukumomin, gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ce ta fara kirkirar hukumar raya yankin Neja Delta bayan wasu ƙalubale da suka dabaibaye yankin.

Na baya-bayan nan ita ce Hukumar Raya yankin Arewa ta Tsakiyar ƙasar nan bayan da ’yan yankin suka nace da yin ƙorafin cewa an mayar da su saniyar ware.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Saukar Farashin Kayan Masarufi A Kaswanni DAGA LARABA: Dalilan Da Al’adar Zanen Fuska Ke Neman Gushewa A Kasar Hausa

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan irin ci-gaban da waɗannan hukumomin raya shiyyoyi za su samar ga al’ummar ƙasa.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja
  • Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa: Barazanar Makiya Kan Iran Ba Zata Yi Nasara Ba
  • NAJERIYA A YAU: Ci-gaban Da Hukumomin Raya Shiyyoyi Za Su Samar
  • Da Dama Sun Rasu Yayin Da NAF Ta Kai Wa ‘Yan Bindiga Hari A Katsina
  • FG Ta Jaddada Bukatar Samarda Sabbin Ka’idojin Visa Domin Taimakawa Kasuwancin A Duniya
  • Kotu ta hana Gwamnatin Tarayya riƙe kuɗin ƙananan hukumomin Kano
  • Gwamnati ta kashe N5bn domin bai wa mata tallafin kiwon awakai a Katsina