IPAC ta amince da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Katsina
Published: 17th, February 2025 GMT
Ƙungiyar Gamayyar Jam’iyyun Siyasa ta Ƙasa (IPAC), reshen Jihar Katsina, ta bayyana amincewarta da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025.
Shugaban ƙungiyar, Alhaji Laminu Lawal Boyi, ya bayyana cewa IPAC ta gamsu da yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana, tare da bai wa dukkanin jam’iyyun siyasa damar shiga zaɓen.
“Baya ga shugabancina a IPAC, ni kuma shugaban jam’iyyar Accord ne, wacce ta shiga zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 34 da kujerun kansiloli 361 a faɗin jihar.
“A matsayina na ɗan takara kuma mai ruwa da tsaki, na gamsu da yadda aka gudanar da zaɓen,” in ji shi.
Da yake yi wa manema labarai jawabi a ofishin IPAC da ke Kofar Durbi, a cikin garin Katsina, tare da wasu jiga-jigan ƙungiyar, Alhaji Laminu ya jaddada cewa a kowane zaɓe dole ne a samu wanda zai yi nasara da kuma wanda ba zai yi ba.
Ya yi kira ga waɗanda ba su yi nasara ba da su karɓi ƙaddara tare da duba gaba, domin siyasa ba ta ƙarewa.
Haka kuma ya shawarci waɗanda suka yi nasara da su fahimci cewa nasarar ba daga ƙarfinsu ko dabara ta fito ba, sai dai hukuncin Allah ne.
Don haka, ya buƙace su da su sauke nauyin da ke kansu cikin adalci, ba tare da nuna bambancin jam’iyya ba, domin yanzu lokaci ne na haɗin kai da ci gaban al’umma gaba ɗaya.
Alhaji Laminu ya ƙara da cewa, “Yanzu siyasa ta wuce, lokaci ne na aiki da tabbatar da ci gaban jama’a.
“Waɗanda suka samu nasara su yi mulki da adalci, su guji nuna bambanci, domin yanzu dukkanin al’umma na kallonsu a matsayin shugabanninsu, ba wai na jam’iyyarsu kaɗai ba.”
Shugaban ya yaba wa dukkanin ’yan takara da jam’iyyun siyasa da suka shiga zaɓen, tare da gode wa hukumomin da suka shirya zaɓen bisa ƙoƙarin da suka yi wajen tabbatar da gudanar da shi cikin zaman lafiya da lumana.
Ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bai wa shugabanni goyon baya domin ci gaban Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Amincewa gamayya Ƙungiya
এছাড়াও পড়ুন:
Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume
Sanatan Kudancin Borno, Ali Ndume, ya bayyana cewa a halin yanzu mayaƙan Boko Haram sun ƙwace yankunan ƙananan hukumomi uku a jihar.
Ndume ya bayyana cewa mayaƙan kungiyar sun kashe fararen hula sanda a 200 da sojoji 100 a sabbin hare-haren da suka kai a sassan jihar a baya-bayan nan.
A wata zantawar da aya yi da ’yan jarida a ƙarshen mako, ɗan Majalisar Dattawan ya ce mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare 252 a daga watan Nuwamban 2024 zuwa yanzu.
Ya bayyana damuwa game da dawowar munanan ayyukan kungiyar a jihar duk kuwa da kokarin da sojoji da sauran hukumomin tsaro ke yi domin murƙushe su.
Abincin karnuka ya fi wanda ake ba mu —Fursunonin Najeriya NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar BornoA sakamako haka ne ya ce sanatoci da ’yan majalisar wakilan Jihar Borno da Gwamna Babagana Zukum, suka yi zama da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin shawo kan matsalar.
Da yake tsokaci kan dawowar hare-haren, Sanata Ndume ya ce, “Wannan abin damuwa ne, duk da cewa sojoji sun halaka ’yan ta’adda sama da 800, su kuma ’yan ta’addan su kashe sama da 500 a sakamakon rikicin ISWAP da Boko Haram.”
Ya ce, “daga watan Nuwambar 2024 zuwa yanzu sun kai hare-hare 252, sun kashe sojoji 100 da fararen hula 500. Yanzu haka kuma kananan hukumomi uku na Jihar Borno — Gudumbari, Maye da Abadam — na hannunsu,” haka zalika sun tarwatsa wasu sansanonin soji da ke wurin.