Aminiya:
2025-03-23@03:05:12 GMT

Jirgin soji ya kashe fararen hula a Katsina

Published: 17th, February 2025 GMT

Wani jirgin sojin Najeriya ya jefa wa fararen hula bom inda ya kashe fararen hula bakwai a yankin Yani  da ke Ƙaramar Hukumar Safana ta Jihar Katsina.

Mamatan sun hada da mutum shida ’yan gida ɗaya, kamar yadda wani shaida ya bayyana.

Hakan na zuwa ne bayan wasu jami’an tsaro da suka hada da ’yan sanda biyu da wani jami’in Rundunar Tsaron Al’umma na jihar (CWC) sun kwanta dama a yayin musayar wuta da ’yan bindiga a Ƙaramar Hukumar a ranar Asabar.

Wani mazaunin Gundumar Zakka da ke Ƙaramar Hukumar, yankin da abin ya faru, ya bayyana cewa an yi arangamar ne bayan zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a jihar ranar Asabar, inda ’yan bindiga suka shirya kai wa masu zaɓe hari a kauyen Zakka.

Bayan samun rahoton shirin harin ne jami’an tsaron suka je domin daƙile ’yan bindigar, inda a garin haka aka yi musayar wuta tsakanin bangarorin. Wani hafsan dan sanda da jami’in CWC sun rasu, daga bisani wani ɗan sanda da ya ji rauni a arangamar ya cika.

Ya bayyana cewa, “bayan nan ne wani jirgin soji ya zo, watakila domin kai wa jami’an tsaron ɗauki. A nan ne ya jefa bom a yankin Yani da ke ƙauyen Zakka, wanda ya halaka  mutum shida ’yan gida ɗaya, ya kuma jikkata wata mata.”

Wannan ba shi ne karon farko ba da jirgin soji ya kai wa fararen hula hari ba a Ƙaramar Hukumar ta Safana.

A watan Yulin shekara ta 2022 wani jirgin soji ya jefa bom a yankin Kunkumi da ke Ƙaramar Hukumar ta Safana, inda ya kashe aƙalla mutum biyu tare da jikkata wasu tara.

Wakilinmu ya yi duk ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sanda da sojoji da ke jihar game da lamarin, amma hakan ya faskara.

Amma dai kafar yaɗa labarai 4 Deutsche Welle (DW) ta ruwaito labarin harin, tana mai ambato wasu shaidu da suka tabbatar da aukuwarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Ƙaramar Hukumar jirgin soji ya fararen hula

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira

Wata gobara da ta tashi a sansanin ’yan gudun hijira na Munna Albadawi da ke ƙaramar hukumar Jere a Jihar Borno, ta lalata wasu gidaje 10 tare da salwantar da rayuwar yaro mai shekara 7 mai suna Abubakar Gargar.

A cewar shugaban sansanin, Babangida Mahmud gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 3:00 asubahin safiyar ranar 20 ga watan Maris, 2025, inda gobarar ta laƙume kayayyakin abinci da tufafi da dai sauran kayayyaki.

Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe

Wanda kawo yanzu ba a tantance adadin asarar da ta haifar ba baya ga salwantar rai guda.

Hukumar kashe gobara ta Jihar Borno tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro sun yi nasarar shawo kan gobarar da ƙyar da jibin goshi bayan da ta yi ɓarna mai yawan gaske.

Tuni dai aka yi wa marigayin jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya shimfiɗa.

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar (SEMA) da sauran hukumomin jin ƙai sun baza jami’ansu a sansanonin don daidaita lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
  • Saree: Filin jirgin saman Ben Gurion ba shi da aminci har sai an kawo karshen yakin Isra’ila a Gaza
  • Gobara ta kashe ɗan shekara 7 a sansanin ’yan gudun hijira
  • Sojoji sun ceto mutum 84 da ’yan bindiga suka sace a Katsina
  • Hajjin Bana: Maniyata 3, 155 Suka Yi Rijista a Kano
  • OIC ta yi Allah wadai da sake dawo da hare-haren yahudawan sahyuniya a kan a zirin Gaza
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara
  • Gobara Ta Babbake Wani Shago A Jihar Kwara
  • Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato