Leadership News Hausa:
2025-04-14@18:14:56 GMT

Tattaunawa Kan Ƙurajen Fuska (Pimples)

Published: 17th, February 2025 GMT

Tattaunawa Kan Ƙurajen Fuska (Pimples)

Kiyaye taruwar maiƙo da kwayoyin cuta a fuska da kirji. Wannan kan dan yi wahala amma ta wadannan dabaru za a samu nasara:

1- Rage maiƙo a cikin abinci. Misali, idan aka soya wani abinci, yana da kyau a tsane mai da mayanin kicin wafif ko tawul ko tushu mai tsabta kafin a ci. Idan an yi haka an rage man kusan da kashi hamsin cikin dari ko ma fiye.

2- Yin amfani da sabulu mai kashe kwayoyin cuta wajen wanke fuskar safe da yamma.

3- Shan kayan itatuwa da cin ganyayyaki a kai –a-kai ya kan tsane maikon cikin jini ya kara karfin garkuwar jiki wajen yakar kwayoyin cuta.

4- Ga wanda wadannan

Dabaru ba su yi musu aiki ba, za su iya zuwa su nemi man shafawa na fuska da kirji mai dauke da sinadarin benzoyl perodide na shafawa safe da yamma bayan an wanke fuska.

5- Idan hakan ta ki wadatarwa sai an je asibiti an hada da karbar magungunan kashe kwayoyin cuta. 6- Ga wadanda wannan ma bai yi aiki ba, akwai dai magunguna masu karfi, har ila yau irin samfurin bitaman ‘A’ da ake kira isotretoin da ake rubutawa a asibiti. Akan samu nasara sosai idan aka jarraba wadannan. Amma ba a ba wa mai juna biyu shi.

7- Ba a so a rika matse kurajen saboda hakan kan iya jawo tabo, an fi so a bar su su fashe da kansu sai a wanke wurin. Allah ya sa mu dace

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kuraje Tattaunawa kwayoyin cuta

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan

Hukumar kula da agaji ta MDD (OCHA) ta bada sanarwan cewa, gwamnatin HKI a yankin yamma da kogin Jordan ta kori Falasdinawa a gidaje 5 a yankin bayan sun rusa gidajensu. Hukumar ta kara da cewa wadanda HKI ta rusa gidajensu a yankin sun hada da yara 19 da da iyayensu 33 maza da mata 6.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto OCHA na cewa tun watan Maris da ya gabata zuwa yanzu, HKI ta rusa gidaje da gine-ginen Fafalsadinawa kimani 100 a yankin yamma da kogin Jordan wadanda suka hada da gabacin birnin Qudus da kuma sauran yankuna, da sunan an gina gidajen ba bisa ka’ida ba.

Banda haka suna kwace gonakin Falasdinawa don ginawa sabin yahudawan da suke shigowa kasar matsugunai.

Labarin y ace, a wasu lokutan yahudawan zasu tilastawa Falasdinawa rusa gidajensu da kansu ko kuma idan sun rusa su da kayan aikinsu su tilastawa Falasdinawan kbiyan kudaden aikin rusawan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza
  • Sharhi: Tattaunawa Zagaye Na Farko Tsakanin Iran Da Amurka A Oman
  • Sin Ta Mika Filayen Wasa Da Ta Yi Wa Gyaran Fuska Ga Senegal
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  •  Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu