Tattaunawa Kan Ƙurajen Fuska (Pimples)
Published: 17th, February 2025 GMT
Kiyaye taruwar maiƙo da kwayoyin cuta a fuska da kirji. Wannan kan dan yi wahala amma ta wadannan dabaru za a samu nasara:
1- Rage maiƙo a cikin abinci. Misali, idan aka soya wani abinci, yana da kyau a tsane mai da mayanin kicin wafif ko tawul ko tushu mai tsabta kafin a ci. Idan an yi haka an rage man kusan da kashi hamsin cikin dari ko ma fiye.
2- Yin amfani da sabulu mai kashe kwayoyin cuta wajen wanke fuskar safe da yamma.
3- Shan kayan itatuwa da cin ganyayyaki a kai –a-kai ya kan tsane maikon cikin jini ya kara karfin garkuwar jiki wajen yakar kwayoyin cuta.
4- Ga wanda wadannan
Dabaru ba su yi musu aiki ba, za su iya zuwa su nemi man shafawa na fuska da kirji mai dauke da sinadarin benzoyl perodide na shafawa safe da yamma bayan an wanke fuska.
5- Idan hakan ta ki wadatarwa sai an je asibiti an hada da karbar magungunan kashe kwayoyin cuta. 6- Ga wadanda wannan ma bai yi aiki ba, akwai dai magunguna masu karfi, har ila yau irin samfurin bitaman ‘A’ da ake kira isotretoin da ake rubutawa a asibiti. Akan samu nasara sosai idan aka jarraba wadannan. Amma ba a ba wa mai juna biyu shi.
7- Ba a so a rika matse kurajen saboda hakan kan iya jawo tabo, an fi so a bar su su fashe da kansu sai a wanke wurin. Allah ya sa mu dace
কীওয়ার্ড: Kuraje Tattaunawa kwayoyin cuta
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda na yi wa budurwar da muka haɗu a Facebook gunduwa-gunduwa —Matashi
Wani matashi da aka kama kan yin gunduwa-gunduwa da budurwarsa da suka haɗu a Facebook bayan ta je ɗakinsa ya bayyana dalilinsa na aikata hakan.
Matashin mai shekaru 29 da ke iƙirarin malumtar addini ya amsa a wurin ’yan sanda masu bincike cewa shi ne ya yi wa gawar budurwar tasa gunduwa-gunduwa.
Ya shaida musu cewa a Facebook ya haɗu da ita, inda daga bisani ta ziyarci ɗakinsa a unguwar Olunlade a garin Ilori, bayan ta je wani biki.
Sai dai ya musanta zargin da ake masa na kashe ɗalibar mai suna Hafsah Yetunde Bello domin yin tsafi.
Jirgin soji ya kashe fararen hula a Katsina Malaman addini sun yi wa ’yan siyasa juyin mulki —Sule Lamiɗo Ku tona asirin ’yan tsubbu —Sarkin Ilori ga malaman addiniA cikin bidiyon tambayoyin da ’yan sanda ke wa matashin mai suna Abdulraham Bello, ya ce bayan zuwan budurwar tasa ne ya je ya sayo mata abinci, bayan ta bayyana masa cewa tana jin yunwa.
Ya shaida wa masu binciken nasa cewa bayan ya dawo daga sayo abincin ne ya iske ta tana shassheka a ɗakin.
“Ba a jima ba sai ta mutu. Ni kuma na tsotsa, babu wanda zan iya zuwa gaya wa ya taimaka min, shi ne ne sassara gawarta na yi mata gunduwa-gunduwa na je na jefar a wata bola a unguwar.
“A rikice nake, ban san abin da zan yi ba, ko tunanin wata hanya ta daban. Amma ban taɓa yin haka ba, wannan ne karon farko,” in ji matashin a ofishin ’yan sanda.
A cikin bidiyon da ya yi jawabin nasa cikin harshen Yarbanci ya bayyana cewa a halin yanzu yana neman gurbin karatu ne a Jami’ar Jihar Kwara (KWASU), Malete.
Mamaciyar dai ɗalibar aikin ƙarshe ce a Kwalejin Koyarwa ta Jihar Kwara.