Aminiya:
2025-03-26@06:29:02 GMT

Kotu ta hana Gwamnatin Tarayya riƙe kuɗin ƙananan hukumomin Kano

Published: 17th, February 2025 GMT

Wata Babbar Kotun Jihar Kano ta haramta wa Gwamnatin Tarayya riƙewa ko kuma yi wa kuɗaɗen ƙananan hukumomi 44 na jihar katsalandan.

Mai Shari’a Musa Ibrahim Muhammad ne ya yanke hukuncin a ranar Litinin, biyo bayan ƙarar da wakilan ƙananan hukumomin jihar suka kai na kare ‘yancinsu na cin gashin kai dangane da kuɗaɗen da Gwamnatin Tarayyar ke ware musu.

Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe Gwamnati ta raba wa mata tallafin awakai na N5bn a Katsina

Wannan shari’ar dai ta samo asali ne bayan da jam’iyyar adawa ta APC ta nemi kotu da ta dakatar da bai wa ƙananan hukumomin jihar kuɗaɗe, bisa zargin tafka maguɗi a zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a watan Oktoban 2024.

Aminiya ta ruwaito cewa, Shugaban  Jam’iyyar APC na Kano, Abdullahi Abbas ne ya jagoranci shigar da ƙarar wadda take ƙalubalantar wasu hukumomin Gwamnatin Tarayya da suka haɗa da Babban Bankin Nijeriya (CBN), Asusun Raba Kuɗi na Tarayya (FAAC), da kuma dukkan ƙananan hukumomi 44 na Kanon.

Sai dai kuma hukuncin da babbar kotun Kano ta yanke ya tabbatar da haƙƙin ƙananan hukumomi na karɓar kudadtensu, tare da hana gwamnatin tarayya ko wasu hukumominta riƙe kuɗaɗen .

A watan Nuwambar bara ce dai Shugaban Ƙungiyar Ƙananan Hukumomi, Ibrahim Muhammad ya jagoranci tawagar masu shigar da ƙara ta hannun lauyansu, Bashir Yusuf Muhammad, suna neman kotun ta hana riƙewa ko jinkirin sakin kuɗin ƙananan hukumomin jihar.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Jihar Kano Kuɗin Ƙananan Hukumomi Gwamnatin Tarayya

এছাড়াও পড়ুন:

Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati

A cewarsa ya zaɓe shi ne bisa la’akari da kwarjininsa da kuma gwanintarsa.

Farfesa Worika yana da digiri na uku a fannin Dokar Muhalli ta Ƙasa da Ƙasa da Man Fetur daga Jami’ar Dundee da ke Birtaniya.

Ya yi aiki a fannoni daban-daban da suka haɗa da harkokin ilimi da kuma ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa.

Naɗinsa yana cikin ƙoƙarin gwamnatin Jihar Ribas na amfani da ƙwararru ‘yan jihar domin samar da zaman lafiya, kwanciyar hankali, da tsaro.

Farfesa Worika ya fito ne daga Ƙaramar Hukumar Okrika a Jihar Ribas.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sudan: RSF ta hana kayan agaji a yankunan da ke a karkashin ikonta
  • Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati
  • Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • UNRWA : hana shigar da kayan agaji Gaza, ya jefa yankin cikin matsanancin hali
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa