Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-16@01:19:15 GMT

An Gudanar Da Taron Bita Na Yini 4 Ga Malaman Tafsiri Da Ke Babura

Published: 18th, February 2025 GMT

An Gudanar Da Taron Bita Na Yini 4 Ga Malaman Tafsiri Da Ke Babura

Cibiyar Malam Bukar mai kula da hidimar al’amuran da suka shafi karantar da Alqur’ani da dake Babura ta gudanar da bitar yini 4 ga Malamai masu Tafsiri da Alarammomi a garin Babura dake Jihar Jigawa.

Da yake jawabi yayin rufe bitar, Shugaban cibiyar, Sheikh Gwani Dr Murtala Bashari yace an shirya bitar ne da nufin kara zaburar da juna da kuma nusar da masu gabatar da tafsirin Alkur’ani kan maida hankali wajen karfafa bin abin Alkur’ani da Sunnar Manzon Allah don kaucewa fadawa miyagun akidu.

Shugaban Wanda jami’in gudanar da Shirin, Dr Ismail Ali kura ya wakilta, ya yabawa mahalarta bitar da jagororinsu bisa kwazonsu.

Shi ma a nasa jawabin, bako na musamman Farfesa Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemu ya ce bitar ta zo a dai dai lokacin da ake fuskantar kalubale na rashin kyakkyawar fahimtar wasu ma’anoni na Alkur’ani da Sunnah.

A don haka, ya bukaci malaman da su kasance a cikin neman ilimi da nazari a koda yaushe.

Hakimin Babura Sarkin Ban Ringim, Alhaji Muhammad Nata’ala Mustapha ya bukaci Malamai da su kara zaburar da iyaye kan muhimmamcin ilimin addinin musulunci ga ‘ya’yansu.

Sai dai kuma, ya koka kan yadda ‘ya’ya mata suka fi maza zuwa islamiyya, knda ya bukaci iyaye su kula domin samun ingantaccen rayuwa.

Daga cikin darussan da malaman suka gabatar yayin bitar sun hada da ilimin da ya kamata mai tafsiri ya samu, da kuma kura-kuran da mai tafsiri ke samu a lokacin karatu.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Babura Jigawa Taron Bita

এছাড়াও পড়ুন:

Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa

Tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ya shirya wani taron bikin cika shekaru 50 da kafuwa tare da gudanar da taron kasa karo na uku.

Taron wanda aka yi wa take da “Ilimi Mai Sauya Rayuwa Don Gaba: Fuskantar Sabbin Kalubale da Buɗe Damar Samun Ci gaba” ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki daga sashen ilimi.

Da take jawabi a wajen taron, Minista a ma’aikatar Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmed Sa’id ta bayyana cewa, a ƙoƙarin da gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ke yi na ƙarfafa tsarin ilimi, ya amince da kashe Naira biliyan 120 don bunƙasa shirin fasaha da koyon sana’o’i (TVET) a Najeriya.

Ministar ta kuma bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta amince da fitar da Naira biliyan 40 domin kammala aikin ɗakin karatu na ƙasa da aka yi watsi da shi, domin tallafawa bincike da cigaban karatu.

Farfesa Suwaiba ta ƙara da cewa, ma’aikatar ilimi ta tarayya ƙarƙashin jagorancin Minista Alausa ta ƙaddamar da Shirin Sabunta Hanyar Ilimi ta Najeriya (NESRI).

“Ina da burin mayar da Najeriya daga tattalin arzikin da ke dogara da albarkatu zuwa tattalin arzikin da ke dogara da ilimi, tare da rage yawan yara da ba sa zuwa makaranta, rage ƙarancin koyo, da samun  ƙara ƙwarewa.”

Yayin da yake buɗe taron, Shugaban Jami’ar Bayero Kano, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya bayyana nasarorin da sashen ya samu, inda ya ce ya samar da manyan mutane kamar ministocin ilimi biyu, shugabannin jami’o’i tara, da matan gwamnan jihar Kano guda uku, da sauran fitattun ’yan Najeriya da suka yi fice a fannoni daban-daban.

Yayin da yake yabawa taken taron da dacewarsa, Farfesa Sagir ya tabbatar da cewa jami’ar tana nan daram wajen tallafawa duk wani shiri da zai ɗaga matsayin ilimi zuwa na ƙasa da ƙasa.

A jawabinsa na maraba, Shugaban tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero Kano (BUK), Dakta Abubakar Ibrahim Hassan, ya jaddada yadda tsangayar ke  kokari wajen shirya harkokin ilimi da na kimiyya.

“Daga cikin nasarorin da Jami’ar BUK ta samu a kwanan nan akwai samun tallafin TETFUND guda biyu da kowanne ya haura naira biliyan 30, tare da lashe wani shirin koyar da harsuna biyu wanda Bankin Raya Musulunci da Hukumar Ilimin Firamare ta Kasa (UBEC) suka dauki nauyi.”

Taron ya yi armashi inda aka bayar da lambar yabo ga fitattun ‘yan Najeriya da suka hada da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da matarsa Farfesa Hafsat, da Minista a ma’aikatar Ilimi ta Jiha Farfesa Suwaiba, tsohuwar Ministar Ilimi Farfesa Rukayya, da Farfesa Isah Yahaya Bunkure da wasu da dama.

Daga Khadija Aliyu 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samarwa Matasa Abun Yi Shi Zai Kawo Ƙarshen Ta’addancin Boko Haram Da ‘Yan Bindiga – Zulum 
  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Al’ummar Babura Sun Karrama Sabon Shugaban Asibitin Koyarwa Na Rasheed Shekoni
  • Ministan Harkokin Noma Na Kasar Iran Ya Kama Hanya Zuwa Kasar Brazil
  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Yi Watsi Da Matsawa Sauran Kasashe Lamba
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Matakin Kare-Karen Harajin Fito Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar
  • Al’ummar Mauritaniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Nuna Adawa Da Yakin Gaza