Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Barazanar makiya a kan kasar Iran da al’ummarta ba ta yi nasara ba

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewa: Gagarumar zanga-zamga da al’ummar Iran suka gudanar a ranar 22 ga watan Bahman ta tabbatar da cewa barazanar makiya a kan Iran da al’ummarta ba ta cimma nasara ko yin tasiri ba.

Jagoran juyin juya halin Musuluncin yayin da yake karbar bakwancin dubban mutane daga lardin gabashin Azarbaijan a Husainiyar Imam Khumaini da ke Tehran fadar mulkin kasar a ranar Litinin din da ta gabata, a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan zagayowar bore mai tarihi na al’ummar Tabriz a ranar 29 ga watan Bahman shekara ta 1356 wanda ya zo daidai da (18 ga watan Fabrairu shekara ta 1978), ya bayyana cewa: Tsare-tsaren barazana ta hanyar wasa da ra’ayin al’umma da watsa sabani kan neman haifar da shakku dangane da kotunan juyin juya halin Musulunci da kuma yada kokwanto game da iya kalubalantar makiya.

Jagoran ya kara da cewa: A wannan taro da ya samu halartar shugaban kasar Masoud Pezeshkian suna jaddada cewa: Makiya suna kokarin tarwatsa al’umma ta hanyar yaudara amma da yardan Allah har yanzu ba su samu nasara ba, kamar yadda suke kokarin girgiza zukatan al’ummar Iran da neman hana matasa samun karfin gwiwar himma da hubbasa a fagen kara ci gaban kasarsu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Jagoran juyin juya halin Musulunci

এছাড়াও পড়ুন:

 Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!

A wata hira da tashar talabijin din, manzon musamman na Amurka a yankin gabas ta tsakiya Steve Witkoff ya rubuta a shafinsa na; X cewa; Sakon da Trump ya aike wa  Tehran ba ta nufin yin barazana.

Manzon na Amurka ya riya cewa;wasikar ta kunshi cewa; Ni shugaban kasa ne mai son zaman lafiya , abinda  nake son bayyanawa kenan, don haka babu bukatar a yi magar yaki. Wajibi ne mu zauna mu tattauna.”

Wittkoff ya kuma ce; Da akwai hanyoyi na bayan fage da ake tatatunawa da Iran.

Har ila yau ya kara da cewa; Abinda Trump yake so shi ne warware sabanin da ake da shi.

Shafin watsa labaru na Axos ya bayyana cewa; Waskiyar da Trump din ya aiko wa Iran ta kunshi ayyana wa’adin watanni biyu na cimma  sabuwar yarjejeniya Nukiliya.

Wannan sabon matsayin na Amurka dai ya zo ne,bayan da mahukunta a jamhuriyar musulunci ta Iran suka bayyana cewa; Amurkan ba za ta sami wani abu daga Iran ba ta hanyar barazana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa
  • Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Jagora: Amurka Ta Kwana Da Sanin Cewa Ba  Wata Riba Da Za Ta Ci Ta Hanyar Yi Wa  Iran Barazana
  • Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu
  • Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri
  • Araghchi : Iran za ta mayar da amsa ga wasikar Trump cikin kwanaki masu zuwa