Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro ta Kano
Published: 18th, February 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaron al’umma ta Jihar Kano mai suna ‘Kano State Security Neighborhood Watch.’
Gwamnan ya sanya hannu kan dokar ne tare da wasu ƙarin dokokin guda biyu, waɗanda suka haɗa da dokar gyara hukumar sufuri ta jihar da kuma wadda ta kafa cibiyar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta jihar.
Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature ya fitar ta ce gwamnan ya amince da dokokin ne a zaman majalisar zartarwar jihar na 25 da ya gudana a fadar gwamnatin jihar.
Hakan na zuwa ne bayan dokar samar da rundunar tsaron ta bi matakan da suka kamata a majalisar dokokin jihar.
Kano dai na fama da matsaloli irin na rikice-rikicen dabanci da ƙwacen waya, lamarin da ya yi sanadiyar ajalin mutane da dama.
Me Abba ya ce?A jawabinsa bayan rarraba hannu dokokin, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ganin an samu ribar dimokuraɗiyya da kuma bunƙasa tattalin arzikin jihar cikin ƙanƙanin lokaci.
Ya kuma jaddada cewa gwamnati ta tsaya tsayin daka a ƙoƙarinta na ɓullo tare da aiwatar da manufofi da tsare-tsare da nufin inganta rayuwar al’ummar Jihar Kano.
Gwamna Yusuf ya bayyana jin daɗinsa dangane da irin goyon baya da haɗin kai da jama’a ke ba su, inda ya buƙaci da su ci gaba da gudanar da ayyukansu domin cimma manufofin gwamnatin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kano State Security Neighborhood Watch Rundunar Tsaron Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
An ruwaito cewa, shirin aikin noman ranin da aka kaddamar a yankin na Lallashi, zai karade hekta 10, wanda kuma sama da kananan manoma 80, za su amfana da shirin kai tsaye.
Bugu da kari, shirin zai taimaka wajen kara samar da girbin amfanin gona mai yawan gaske tare kuma da kara bunkasa tattalin arzikin jihar baki-daya.
Malam Aliyu Musa, da yake yin jawabi a madadin sauran manoman da ke yankin ya bayyana cewa, samar da shirin a yankin da gwamnatin jihar ta yi, tamkar zuba hannun jari ne.
A cewarsa, al’ummar yankin za su ci gaba da yin addu’a, domin shirin ya dore tare kuma da ganin an kara fadada shi, don su ma sauran yankunan jihar su amfana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp