Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
Published: 21st, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kano ta dauki wani gagarumin mataki na bunkasa ilimin addinin musulunci a jihar ta hanyar hada hannu da kungiyar Agaji ta Musulunci da ke Birtaniya, wato Muslim Charity For United Kingdom a turance.
Wannan haɗin gwiwar na nufin tallafa wa makarantun Islamiyya da kayayyakin koyon ilimi na zamani, da sauransu.
A cewar daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, wannan shiri ya yi daidai da kokarin da gwamnati ke yi na karfafa fannin ilimi.
Haɗin gwiwar zai magance matsalolin da ke addabar ilimin addinin Islama, da tabbatar da cewa makarantun Islamiyya sun sami tallafin da ya dace don samu ingantaccen yanayin karatu da koyarwa.
Ya yi nuni da cewa, Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Makoda, ya bayyana fatan cewa, wannan hadin gwiwa zai inganta ilimin addinin Musulunci, musamman a tsarin makarantun Islamiyya.
Ya ce, shirin zai mayar da hankali ne wajen samar da kayayyakin koyo na zamani domin inganta kwazon dalibai.
Da take jawabi a madadin tawagar, shugabar kungiyar agaji ta addininMusuluncida ke Birtaniya, Dr. Samira Abubakar Abdullahi, ta bayyana cewa kungiyar na aiki tukuru a Najeriya domin tallafawa harkokin ilimi da kiwon lafiya.
Ta bayyana cewa gudummawar da suke bayarwa sun hada da shirye-shiryen gyara makarantu, ayyukan ci gaban ilimi, da ayyukan kiwon lafiya.
“Mun zo ma’aikatar don tattaunawa kan bangarorin haɗin gwiwa da kuma yi wa kwamishina bayani game da ayyukanmu,” inji ta.
Kungiyar agajin tana aiki tukuru a Najeriya don tallafawa ayyukan ilimi da kiwon lafiya.
Daga Khadija Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kungiyar Agaji
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja
Ana fargabar matafiya da dama sun rasu bayan kifewar wani kwalekwale ɗauke da ’yan kasuwa a yankin Kogin Neja.
Hatsarin kwalekwalen ya auku ne ƙauyen Sokun da ke yankin Ƙaramar Hukumar Lapai, a sakamakon iska mai ƙarfi da ta haddasa juyawar igiyar ruwan.
Shaidu sun ce hatsarin ya auku ne a yayin da kwalekwalen ke ɗauke da fasinjoji da kuma buhunan shinkafa kimanin 200 daga ƙauyen Bugge na Jihar Kogi a zuwa ƙauyen Sokun na Jihar Neja a ranar Laraba da dare.
Wani mazaunin yankin, Baba Alhassan, ya shaida wa wakilinmu cewa, ba a kai ga tantance ainihin yawan fasinjojin da ke cikin kwalwkwalen a lokacin da lamarin ya faru ba, amma an yi asarar duk buhunan shinkafar a hastarin.
NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan NajeriyaYa bayyana cewa daga cikin mamatan har da wani mai sana’ar POS da ƙaninsa ’yan asalin ƙauyen Alaba da ke Ƙaramar Hukumar Lapai
Daraktan Hukumar ba da Agajin Gaggawa na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa ana ci gaba da aikin ceto da ƙoƙarin gano ainihin musabbabin hatsarin da kuma irin asarar da ta haifar.
Mazauna yankin sun bayyana cewa, “Sufurin ruwa shi ne kaɗai hanyar da ta rage da muke amfani da ita domin kai kayanmu kasuwanni saboda hanyar ta yi mummunan lalacewa.”
Wata ’yar kasuwa a yankin mai suna Fatima Muhammad, ta bayyana cewa, saboda nisan tafiyar, fasinjoji sukan yi tafiyar dare domin su isa kasuwa washegari da safe.
Fatima ta ce, “Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne sufuri. Da kwalekwale muka dogara wajen kai kayanmu kasuwa. Wani lokaci kwalekwalen na ɗaukar lodi fiye da kima. Sai ka ga kwalekwale mai ƙarfin ɗaukar mutane 100 ya kwashi sama da haka. Amma ban ga laifin fasinjojin ba, musamman masu son su isa da wuri.”
Jama’ar yankin sun yi kira ga Gwamnatin Jihar Neja da ta Tarayya da su samar da wadatattun rigunan kariya da jiragen ruwa na zamani sannan su aiwatar da tsauraran hukunci kan masu karya doka.